< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
Elihu poursuivit encore son discours, et dit:
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
As-tu pensé rendre ta cause bonne, [quand] tu as dit: Ma justice [est] au-dessus de celle du [Dieu] Fort?
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
Si tu demandes de quoi elle te profitera, [disant]: Que m'en reviendra-t-il, de même que de mon péché?
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
Je te répondrai en ces termes, et à tes amis qui sont avec toi.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Regarde les cieux, et les contemple; vois les nuées, elles sont plus hautes que toi.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
Si tu pèches, quel mal fais-tu à Dieu? et quand tes péchés se multiplieront, quel mal en recevra-t-il?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
Si tu es juste, que lui donnes-tu? et qu'est-ce qu'il reçoit de ta main?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
C'est à un homme, comme tu es, que ta méchanceté [peut nuire]; et c'est au fils d'un homme que ta justice [peut être utile].
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
On fait crier les opprimés par la grandeur [des maux qu'on leur fait]; ils crient à cause de la violence des grands.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
Et on ne dit point: où est le Dieu qui m'a fait, [et] qui donne de quoi chanter pendant la nuit;
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
Qui nous rend plus éclairés que les animaux de la terre, et plus intelligents que les oiseaux des cieux?
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
On crie donc à cause de la fierté des méchants; mais Dieu ne les exauce point.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Cependant [tu ne dois pas dire] que ce soit en vain; que le [Dieu] Fort n'écoute point, et que le Tout-puissant n'y a nul égard.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
Encore moins lui dois-tu dire; tu ne le vois point; car le jugement est devant lui; attends-le donc.
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
Mais maintenant, ce n'est rien ce que sa colère exécute, et il n'est point entré fort avant en connaissance de toutes les choses que tu as faites.
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
Job donc a ouvert sans raison sa bouche [pour se plaindre], et il a entassé paroles sur paroles, sans connaissance.

< Ayuba 35 >