< Ayuba 35 >
Et Elihou, continuant dit:
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
Qu'as-tu pensé obtenir d'un jugement? Qui es-tu, toi qui as osé dire: Je suis juste devant le Seigneur?
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
Quand tu dis: En quoi pécherai-je?
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
Vous allez entendre la réponse, toi et tes trois amis.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Lève les yeux au ciel et regarde; les nuées t'enseigneront combien les choses d'en haut sont loin de toi.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
Si tu pèches, quel danger court le Seigneur? Si tes fautes sont nombreuses, que pourras-tu faire contre lui?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
Si tu es juste, qu'en revient-il à Dieu? Que prendra-t-il de ta main?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
C'est l'homme, ton semblable, que ton impiété touche; c'est le fils de l'homme qu'intéresse ta justice.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
Les gens de mauvaise foi se plaindront de tout; ils crieront à l'oppression, à la violence.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
Et nul d'entre eux n'a dit: Où est Dieu, mon créateur, qui a mis en ordre les astres de la nuit,
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
Qui m'a distingué des bêtes de la terre et des oiseaux du ciel?
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
Ils crieront et il n'entendra pas; et ils se plaindront des outrages des méchants.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Mais le Seigneur, le seul Tout-Puissant refuse de jeter un regard sur les choses vaines.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
Il voit tous ceux qui commettent des iniquités, et il me sauvera; soumets-toi à sa justice; puisses-tu le louer tel qu'il est maintenant pour toi.
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
Car nul n'a le droit d'examiner sa colère ni de présumer qu'il fait quelque faux pas.
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
Job a donc témérairement ouvert la bouche, et son courroux provient de son ignorance des choses.