< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
Et Élihu reprit la parole et dit:
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
Penses-tu que ceci soit fondé, que tu aies dit: Je suis plus juste que Dieu?
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
Car tu as demandé quel profit tu en as: Quel avantage en ai-je de plus que si j’avais péché?
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
Je te répliquerai, moi, par des paroles, et à tes amis avec toi:
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Regarde les cieux et vois, et contemple les nuées: elles sont plus hautes que toi.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
Si tu pèches, quel tort lui causes-tu? et si tes transgressions se multiplient, que lui as-tu fait?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
Si tu es juste, que lui donnes-tu, ou que reçoit-il de ta main?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
Pour un homme comme toi ta méchanceté [peut être quelque chose], et pour un fils d’homme, ta justice.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
On crie à cause de la multitude des oppressions, et on appelle au secours à cause du bras des grands;
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
Et on ne dit pas: Où est Dieu, mon créateur, qui donne des chants de joie dans la nuit,
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
Qui nous rend plus instruits que les bêtes de la terre, et plus sages que les oiseaux des cieux?
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
Alors on crie, et il ne répond pas, à cause de l’orgueil des méchants.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Certainement ce qui est vanité Dieu ne l’écoute pas, et le Tout-puissant ne le regarde pas.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
Quoique tu dises que tu ne le vois pas, le jugement est devant lui; attends-le donc.
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
Et maintenant, si sa colère n’a pas encore visité, [Job] ne connaît-il pas [sa] grande arrogance?
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
Et Job ouvre sa bouche vainement; il entasse des paroles sans science.

< Ayuba 35 >