< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
Moreover Elihu answered,
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
“Do you think this to be your right, or do you say, ‘My righteousness is more than God’s,’
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
that you ask, ‘What advantage will it be to you? What profit will I have, more than if I had sinned?’
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
I will answer you, and your companions with you.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Look to the skies, and see. See the skies, which are higher than you.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
If you have sinned, what effect do you have against him? If your transgressions are multiplied, what do you do to him?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
If you are righteous, what do you give him? Or what does he receive from your hand?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
Your wickedness may hurt a man as you are, and your righteousness may profit a son of man.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
“By reason of the multitude of oppressions they cry out. They cry for help by reason of the arm of the mighty.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
But no one says, ‘Where is God my Maker, who gives songs in the night,
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
who teaches us more than the animals of the earth, and makes us wiser than the birds of the sky?’
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
There they cry, but no one answers, because of the pride of evil men.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Surely God will not hear an empty cry, neither will the Almighty regard it.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
How much less when you say you don’t see him. The cause is before him, and you wait for him!
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
But now, because he has not visited in his anger, neither does he greatly regard arrogance,
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
therefore Job opens his mouth with empty talk, and he multiplies words without knowledge.”

< Ayuba 35 >