< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
Then Elihu also said this:
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
“[Job, ] do you think that what you said is right/correct? You say, ‘God knows that I am innocent,’
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
and you say [to God], ‘What good have I received for not sinning? What benefit have I received from that?’ [DOU, RHQ]
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
[Well, ] I will answer you, and I will answer your three friends, too.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
“[Job], look up at the sky; look at the clouds that are high above you and realize [that God is far above everything].
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
If you have sinned, that does not [RHQ] harm God at all. If many times you do things that are wrong, that certainly does not [RHQ] affect him [DOU].
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
And if you are righteous, does that help God? No, he is not benefited by anything that you do [DOU].
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
It is other people who suffer because of the wicked things that you do, but by doing good things for people, you help them.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
“People cry out because of the many things that people do to others to (oppress them/treat them cruelly); they call for help because of the things that powerful people do [MTY] to them.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
But (no one/none of them) calls out [to God], saying ‘Why does God, my creator, [not help me]? He [should] enable me to sing [joyful] songs, [instead of very sad songs, ] during the night.
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
He [should be able to] teach us more than all the wild animals do; he [should] enable us to become wiser than [all] the birds are!’
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
People cry out [for help], but God does not answer them, because those who cry out are proud and evil people.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
It is useless for them to cry out, because God, the Almighty One, does not pay any attention to what they say.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
So, when you complain that you cannot see God, and you tell him that you are waiting for him [to decide whether or not you should be punished for what you have done], God will not listen to you, either!
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
Furthermore, [you say that] because he does not pay attention when people commit sins, he does not become angry and punish them.
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
You say things that are useless; you say a lot of things without knowing [what you are talking about].”

< Ayuba 35 >