< Ayuba 35 >
Then commenced Elihu, and said,
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
Dost thou deem this to be just, that thou hast said, “My righteousness is more than God's?”
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
For thou sayest, “What benefit will it be unto thee? what more profit shall I have, than if I had sinned?”
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
I will truly reply unto thee with words, and unto thy friends with thee.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Look unto the heavens, and see; and gaze on the skies which are higher than thou.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
If thou sin, what dost thou effect against him? and if thy transgressions be multiplied, what canst thou do unto him?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
If thou be righteous, what givest thou him? or what doth he accept out of thy hand?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
A man like thyself thy wickedness may reach, and a son of earth thy righteousness.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
By reason of the multitude of oppressions [the wicked] cause men to cry: these complain aloud because of the arm of the mighty.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
But [man] saith not, Where is God my maker, who bestoweth joyful songs even in the night;
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
Who teacheth us more than the beasts of the earth, and maketh us wiser than the fowls of the heavens?
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
There do they cry, but he answereth not: because of the pride of evil men.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Only what is false will God not hear, nor will the Almighty regard it.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
Although thou sayest, thou canst not see him: yet the decision is before him; and do thou wait for him.
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
But now, because his anger hath punished nothing, shall he not greatly take cognizance of the multitude of sins?
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
But Job openeth wide his mouth for nought: without knowledge he heapeth up words.