< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
Elihu spoke moreover, and said,
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
Think you this to be right, that you said, My righteousness is more than God's?
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
For you said, What advantage will it be unto you? and, What profit shall I have, if I be cleansed from my sin?
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
I will answer you, and your companions with you.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Look unto the heavens, and see; and behold the clouds which are higher than you.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
If you sin, what do you against him? or if your transgressions be multiplied, what do you unto him?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
If you be righteous, what give you him? or what receives he of your hand?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
Your wickedness may hurt a man as you are; and your righteousness may profit the son of man.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
By reason of the multitude of oppressions they make the oppressed to cry: they cry out by reason of the arm of the mighty.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
But none says, Where is God my maker, who gives songs in the night;
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
Who teaches us more than the beasts of the earth, and makes us wiser than the fowls of heaven?
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
There they cry, but none gives answer, because of the pride of evil men.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Surely God will not hear vanity, neither will the Almighty regard it.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
Although you say you shall not see him, yet judgment is before him; therefore trust you in him.
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
But now, because it is not so, he has visited in his anger; yet he knows it not in great extremity:
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
Therefore does Job open his mouth in vain; he multiplies words without knowledge.

< Ayuba 35 >