< Ayuba 35 >
Then Elihu continued, saying,
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
“Do you think it's honest to claim you are right before God?
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
And you ask, ‘What benefit do I get? What good has it done me by not sinning?’
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
I'll tell you, and your friends too!
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Just look up at the sky and see. Observe the clouds high above you.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
If you sin, how does that harm God? How do your many sins affect God?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
If you do what's right, what good are you doing for him?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
No—your sins only affect people like yourself, and whatever good you do only affects them too.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
People cry out because of terrible persecution; they call for someone to save them from their oppressors.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
But no one asks, ‘Where is the God my maker, the one who gives songs in the night,
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
who teaches us more than the animals, and makes us wiser than the birds?’
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
When they call out for help, God doesn't answer because they are proud and evil people.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
God doesn't listen to their empty cries; the Almighty doesn't pay them any attention.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
How much less will God hear you when you say he can't see you? Your case is before him, so you have to wait for him.
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
You're saying that God doesn't punish people in his anger and pays little attention to sin.
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
You, Job, are talking nonsense, making long speeches when you know nothing!”