< Ayuba 35 >
Moreover Eliu spoke these words:
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
Doth thy thought seem right to thee, that thou shouldst say: I am more just than God?
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
For thou saidst: That which is right doth not please thee: or what will it profit thee if I sin?
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
Therefore I will answer thy words, and thy friends with thee.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Look up to heaven and see, and behold the sky, that it is higher than thee.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
If thou sin, what shalt thou hurt him? and if thy iniquities be multiplied, what shalt thou do against him?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
And if thou do justly, what shalt thou give him, or what shall he receive of thy hand?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
Thy wickedness may hurt a man that is like thee: and thy justice may help the son of man.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
By reason of the multitude of oppressions they shall cry out: and shall wail for the violence of the arm of tyrants.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
And he hath not said: Where is God, who made me, who hath given songs in the night?
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
Who teacheth us more than the beasts of the earth, and instructeth us more than the fowls of the air.
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
There shall they cry, and he will not hear, because of the pride of evil men.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
God therefore will not hear in vain, and the Almighty will look into the causes of every one.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
Yea when thou shalt say: He considereth not: be judged before him, and expect him.
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
For he doth not now bring on his fury, neither doth he revenge wickedness exceedingly.
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
Therefore Job openeth his mouth in vain, and multiplieth words without knowledge.