< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
Moreover Elihu answered and said,
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
Thinkest thou this to be [thy] right, [Or] sayest thou, My righteousness is more than God’s,
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
That thou sayest, What advantage will it be unto thee? [And], What profit shall I have, more than if I had sinned?
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
I will answer thee, And thy companions with thee.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Look unto the heavens, and see; And behold the skies, which are higher than thou.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
If thou hast sinned, what effectest thou against him? And if thy transgressions be multiplied, what doest thou unto him?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
If thou be righteous, what givest thou him? Or what receiveth he of thy hand?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
Thy wickedness [may hurt] a man as thou art; And thy righteousness [may profit] a son of man.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
By reason of the multitude of oppressions they cry out; They cry for help by reason of the arm of the mighty.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
But none saith, Where is God my Maker, Who giveth songs in the night,
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
Who teacheth us more than the beasts of the earth, And maketh us wiser than the birds of the heavens?
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
There they cry, but none giveth answer, Because of the pride of evil men.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Surely God will not hear an empty [cry], Neither will the Almighty regard it.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
How much less when thou sayest thou beholdest him not, The cause is before him, and thou waitest for him!
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
But now, because he hath not visited in his anger, Neither doth he greatly regard arrogance;
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
Therefore doth Job open his mouth in vanity; He multiplieth words without knowledge.

< Ayuba 35 >