< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
Elihu nastavi svoju besjedu i reče:
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
“Zar ti misliš da pravo svoje braniš, da pravednost pred Bogom dokazuješ,
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
kada mu kažeš: 'Što ti je to važno, i ako griješim, što ti činim time?'
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
Na sve to ja ću odgovorit' tebi i prijateljima tvojim ujedno.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Po nebu se obazri i promatraj! Gledaj oblake: od tebe su viši!
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
Ako griješiš, što si mu uradio, prijestupom svojim što si mu zadao?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
Ako si prav, što si dodao njemu i što iz ruke tvoje on dobiva?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
Opakost tvoja tebi slične pogađa i pravda tvoja čovjeku koristi.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
Ali kad ispod teškog stenju jarma, kad vapiju na nasilje moćnika,
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
nitko ne kaže: 'Gdje je Bog, moj tvorac, koji noć pjesmom veselom ispunja,
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
umnijim nas od zvijeri zemskih čini i mudrijima od ptica nebeskih?'
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
Tad vapiju, al' on ne odgovara poradi oholosti zlikovaca.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Ali kako je isprazno tvrditi da Bog njihove ne čuje vapaje, da pogled na njih ne svraća Svesilni!
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
A kamoli tek kada ti govoriš: 'On ne vidi mene, parnica moja pred njime stoji, a ja na nj još čekam.'
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
Ili: 'Njegova srdžba ne kažnjava, nimalo on za prijestupe ne mari.'
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
Isprazno tada otvara Job usta i besjede gomila nerazumne.”

< Ayuba 35 >