< Ayuba 31 >

1 “Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
J’avais fait un pacte avec mes yeux, Et je n’aurais pas arrêté mes regards sur une vierge.
2 Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
Quelle part Dieu m’eût-il réservée d’en haut? Quel héritage le Tout-Puissant m’eût-il envoyé des cieux?
3 Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
La ruine n’est-elle pas pour le méchant, Et le malheur pour ceux qui commettent l’iniquité?
4 Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
Dieu n’a-t-il pas connu mes voies? N’a-t-il pas compté tous mes pas?
5 “In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
Si j’ai marché dans le mensonge, Si mon pied a couru vers la fraude,
6 Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
Que Dieu me pèse dans des balances justes, Et il reconnaîtra mon intégrité!
7 In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
Si mon pas s’est détourné du droit chemin, Si mon cœur a suivi mes yeux, Si quelque souillure s’est attachée à mes mains,
8 bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
Que je sème et qu’un autre moissonne, Et que mes rejetons soient déracinés!
9 “In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
Si mon cœur a été séduit par une femme, Si j’ai fait le guet à la porte de mon prochain,
10 sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
Que ma femme tourne la meule pour un autre, Et que d’autres la déshonorent!
11 Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
Car c’est un crime, Un forfait que punissent les juges;
12 Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
C’est un feu qui dévore jusqu’à la ruine, Et qui aurait détruit toute ma richesse.
13 “In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
Si j’ai méprisé le droit de mon serviteur ou de ma servante Lorsqu’ils étaient en contestation avec moi,
14 me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
Qu’ai-je à faire, quand Dieu se lève? Qu’ai-je à répondre, quand il châtie?
15 Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
Celui qui m’a créé dans le ventre de ma mère ne l’a-t-il pas créé? Le même Dieu ne nous a-t-il pas formés dans le sein maternel?
16 “In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
Si j’ai refusé aux pauvres ce qu’ils demandaient, Si j’ai fait languir les yeux de la veuve,
17 in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
Si j’ai mangé seul mon pain, Sans que l’orphelin en ait eu sa part,
18 amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
Moi qui l’ai dès ma jeunesse élevé comme un père, Moi qui dès ma naissance ai soutenu la veuve;
19 In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
Si j’ai vu le malheureux manquer de vêtements, L’indigent n’avoir point de couverture,
20 kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
Sans que ses reins m’aient béni, Sans qu’il ait été réchauffé par la toison de mes agneaux;
21 in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
Si j’ai levé la main contre l’orphelin, Parce que je me sentais un appui dans les juges;
22 bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
Que mon épaule se détache de sa jointure, Que mon bras tombe et qu’il se brise!
23 Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
Car les châtiments de Dieu m’épouvantent, Et je ne puis rien devant sa majesté.
24 “In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
Si j’ai mis dans l’or ma confiance, Si j’ai dit à l’or: Tu es mon espoir;
25 in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
Si je me suis réjoui de la grandeur de mes biens, De la quantité des richesses que j’avais acquises;
26 In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
Si j’ai regardé le soleil quand il brillait, La lune quand elle s’avançait majestueuse,
27 zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
Et si mon cœur s’est laissé séduire en secret, Si ma main s’est portée sur ma bouche;
28 Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
C’est encore un crime que doivent punir les juges, Et j’aurais renié le Dieu d’en haut!
29 “In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
Si j’ai été joyeux du malheur de mon ennemi, Si j’ai sauté d’allégresse quand les revers l’ont atteint,
30 ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
Moi qui n’ai pas permis à ma langue de pécher, De demander sa mort avec imprécation;
31 in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
Si les gens de ma tente ne disaient pas: Où est celui qui n’a pas été rassasié de sa viande?
32 Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
Si l’étranger passait la nuit dehors, Si je n’ouvrais pas ma porte au voyageur;
33 in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
Si, comme les hommes, j’ai caché mes transgressions, Et renfermé mes iniquités dans mon sein,
34 domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
Parce que j’avais peur de la multitude, Parce que je craignais le mépris des familles, Me tenant à l’écart et n’osant franchir ma porte…
35 (“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
Oh! Qui me fera trouver quelqu’un qui m’écoute? Voilà ma défense toute signée: Que le Tout-Puissant me réponde! Qui me donnera la plainte écrite par mon adversaire?
36 Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
Je porterai son écrit sur mon épaule, Je l’attacherai sur mon front comme une couronne;
37 Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
Je lui rendrai compte de tous mes pas, Je m’approcherai de lui comme un prince.
38 “In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
Si ma terre crie contre moi, Et que ses sillons versent des larmes;
39 in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
Si j’en ai mangé le produit sans l’avoir payée, Et que j’aie attristé l’âme de ses anciens maîtres;
40 bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.
Qu’il y croisse des épines au lieu de froment, Et de l’ivraie au lieu d’orge! Fin des paroles de Job.

< Ayuba 31 >