< Ayuba 28 >

1 Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
Il y a pour l’argent une mine d’où on le fait sortir, Et pour l’or un lieu d’où on l’extrait pour l’affiner;
2 Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
Le fer se tire de la poussière, Et la pierre se fond pour produire l’airain.
3 Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
L’homme fait cesser les ténèbres; Il explore, jusque dans les endroits les plus profonds, Les pierres cachées dans l’obscurité et dans l’ombre de la mort.
4 Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
Il creuse un puits loin des lieux habités; Ses pieds ne lui sont plus en aide, Et il est suspendu, balancé, loin des humains.
5 Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
La terre, d’où sort le pain, Est bouleversée dans ses entrailles comme par le feu.
6 akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
Ses pierres contiennent du saphir, Et l’on y trouve de la poudre d’or.
7 Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
L’oiseau de proie n’en connaît pas le sentier, L’œil du vautour ne l’a point aperçu;
8 Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
Les plus fiers animaux ne l’ont point foulé, Le lion n’y a jamais passé.
9 Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
L’homme porte sa main sur le roc, Il renverse les montagnes depuis la racine;
10 Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
Il ouvre des tranchées dans les rochers, Et son œil contemple tout ce qu’il y a de précieux;
11 Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
Il arrête l’écoulement des eaux, Et il produit à la lumière ce qui est caché.
12 Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
Mais la sagesse, où se trouve-t-elle? Où est la demeure de l’intelligence?
13 Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
L’homme n’en connaît point le prix; Elle ne se trouve pas dans la terre des vivants.
14 Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
L’abîme dit: Elle n’est point en moi; Et la mer dit: Elle n’est point avec moi.
15 Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
Elle ne se donne pas contre de l’or pur, Elle ne s’achète pas au poids de l’argent;
16 Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
Elle ne se pèse pas contre l’or d’Ophir, Ni contre le précieux onyx, ni contre le saphir;
17 Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
Elle ne peut se comparer à l’or ni au verre, Elle ne peut s’échanger pour un vase d’or fin.
18 Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
Le corail et le cristal ne sont rien auprès d’elle: La sagesse vaut plus que les perles.
19 Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
La topaze d’Éthiopie n’est point son égale, Et l’or pur n’entre pas en balance avec elle.
20 “To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
D’où vient donc la sagesse? Où est la demeure de l’intelligence?
21 An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
Elle est cachée aux yeux de tout vivant, Elle est cachée aux oiseaux du ciel.
22 Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
Le gouffre et la mort disent: Nous en avons entendu parler.
23 Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
C’est Dieu qui en sait le chemin, C’est lui qui en connaît la demeure;
24 Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
Car il voit jusqu’aux extrémités de la terre, Il aperçoit tout sous les cieux.
25 Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
Quand il régla le poids du vent, Et qu’il fixa la mesure des eaux,
26 Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
Quand il donna des lois à la pluie, Et qu’il traça la route de l’éclair et du tonnerre,
27 sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
Alors il vit la sagesse et la manifesta, Il en posa les fondements et la mit à l’épreuve.
28 Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”
Puis il dit à l’homme: Voici, la crainte du Seigneur, c’est la sagesse; S’éloigner du mal, c’est l’intelligence.

< Ayuba 28 >