< Ayuba 27 >

1 Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
ויסף איוב שאת משלו ויאמר׃
2 “Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
חי אל הסיר משפטי ושדי המר נפשי׃
3 Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
כי כל עוד נשמתי בי ורוח אלוה באפי׃
4 bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
אם תדברנה שפתי עולה ולשוני אם יהגה רמיה׃
5 Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
חלילה לי אם אצדיק אתכם עד אגוע לא אסיר תמתי ממני׃
6 Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
בצדקתי החזקתי ולא ארפה לא יחרף לבבי מימי׃
7 “Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
יהי כרשע איבי ומתקוממי כעול׃
8 Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
כי מה תקות חנף כי יבצע כי ישל אלוה נפשו׃
9 Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
הצעקתו ישמע אל כי תבוא עליו צרה׃
10 Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
אם על שדי יתענג יקרא אלוה בכל עת׃
11 “Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
אורה אתכם ביד אל אשר עם שדי לא אכחד׃
12 Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
הן אתם כלכם חזיתם ולמה זה הבל תהבלו׃
13 “Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
זה חלק אדם רשע עם אל ונחלת עריצים משדי יקחו׃
14 Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
אם ירבו בניו למו חרב וצאצאיו לא ישבעו לחם׃
15 Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
שרידו במות יקברו ואלמנתיו לא תבכינה׃
16 Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
אם יצבר כעפר כסף וכחמר יכין מלבוש׃
17 abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
יכין וצדיק ילבש וכסף נקי יחלק׃
18 Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
בנה כעש ביתו וכסכה עשה נצר׃
19 Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
עשיר ישכב ולא יאסף עיניו פקח ואיננו׃
20 Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
תשיגהו כמים בלהות לילה גנבתו סופה׃
21 Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
ישאהו קדים וילך וישערהו ממקמו׃
22 Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
וישלך עליו ולא יחמל מידו ברוח יברח׃
23 Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”
ישפק עלימו כפימו וישרק עליו ממקמו׃

< Ayuba 27 >