< Ayuba 23 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Eyüp şöyle yanıtladı:
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
“Bugün de acı acı yakınacağım, İniltime karşın Tanrı'nın üzerimdeki eli ağırdır.
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
Keşke O'nu nerede bulacağımı bilseydim, Tahtına varabilseydim!
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
Davamı önünde dile getirir, Kanıtlarımı art arda sıralardım.
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
Bana vereceği yanıtı öğrenir, Ne diyeceğini anlardım.
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
Eşsiz gücüyle bana karşı mı çıkardı? Hayır, yalnızca dinlerdi beni.
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
Haklı kişi davasını oraya, O'nun önüne getirebilirdi, Ben de yargılanmaktan sonsuza dek kurtulurdum.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
“Doğuya gitsem orada değil, Batıya gitsem O'nu bulamıyorum.
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
Kuzeyde iş görse O'nu seçemiyorum, Güneye dönse O'nu göremiyorum.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
Ama O tuttuğum yolu biliyor, Beni sınadığında altın gibi çıkacağım.
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
Adımlarını yakından izledim, Sapmadan yolunu tuttum.
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
Ağzından çıkan buyruklardan ayrılmadım, Günlük ekmeğimden çok ağzından çıkan sözlere değer verdim.
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
“O tek başınadır, kim O'nu caydırabilir? Canı ne isterse onu yapar.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
Benimle ilgili kararını yerine getirir, Daha nice tasarısı vardır.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
Bu yüzden dehşete düşerim huzurunda, Düşündükçe korkarım O'ndan.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
Tanrı cesaretimi kırdı, Her Şeye Gücü Yeten beni yıldırdı.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
Karanlık beni susturamadı, Yüzümü örten koyu karanlık.

< Ayuba 23 >