< Ayuba 23 >
1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Y RESPONDIÓ Job, y dijo:
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
Hoy también hablaré con amargura; que es más grave mi llaga que mi gemido.
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
¡Quién me diera el saber dónde hallar á Dios! yo iría hasta su silla.
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
Ordenaría juicio delante de él, y henchiría mi boca de argumentos.
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
Yo sabría lo que él me respondería, y entendería lo que me dijese.
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
¿Pleitearía conmigo con grandeza de fuerza? No: antes él la pondría en mí.
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
Allí el justo razonaría con él: y escaparía para siempre de mi juez.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
He aquí yo iré al oriente, y no lo [hallaré]; y al occidente, y no lo percibiré:
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
Si al norte él obrare, yo no lo veré; al mediodía se esconderá, y no lo veré.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
Mas él conoció mi camino: probaráme, y saldré como oro.
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
Mis pies tomaron su rastro; guardé su camino, y no me aparté.
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
Del mandamiento de sus labios nunca me separé; guardé las palabras de su boca más que mi comida.
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
Empero si él [se determina] en una cosa, ¿quién lo apartará? Su alma deseó, é hizo.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
El pues acabará lo que ha determinado de mí: y muchas cosas como estas hay en él.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
Por lo cual yo me espanto en su presencia: consideraré, y temerélo.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
Dios ha enervado mi corazón, y hame turbado el Omnipotente.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
¿Por qué no fuí yo cortado delante de las tinieblas, y cubrió con oscuridad mi rostro?