< Ayuba 23 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Y respondió Job, y dijo:
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
Hoy también hablaré con amargura, y será más grave mi llaga que mi gemido.
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
¡Quién diese que le conociese, y le hallase! yo iría hasta su trono.
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
Ordenaría juicio delante de él, y mi boca henchiría de argumentos.
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
Yo sabría lo que él me respondería, y entendería lo que me dijese.
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
¿Pleitearía conmigo con multitud de fuerza? No: antes él la pondría en mí.
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
Allí el recto disputaría con él; y escaparía para siempre de él que me condena.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
He aquí, yo iré al oriente, y no le hallaré, y al occidente, y no le entenderé.
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
Si al norte él obrare, yo no le veré: al mediodía se esconderá, y no le veré.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
Mas él conoció mi camino: probóme, y salí como oro.
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
Mis pies tomaron su rastro: guardé su camino, y no me aparté.
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
Del mandamiento de sus labios nunca me quité: las palabras de su boca guardé más que mi comida.
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
Y si él se determina en una cosa, ¿quién le apartará? Su alma deseó, e hizo.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
Por tanto él acabará lo que ha determinado de mí; y muchas cosas como estas hay en él.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
Por lo cual yo me espantaré delante de su rostro: consideraré, y temerle he.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
Dios ha enternecido mi corazón, y el Omnipotente me ha espantado.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
¿Por qué yo no fui cortado delante de las tinieblas, y cubrió con oscuridad mi rostro?

< Ayuba 23 >