< Ayuba 23 >
1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Job respondió:
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
Aun hoy es amarga mi queja, pues mi llaga agrava mis gemidos.
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
¡Ojalá me concediera saber dónde hallarlo! Yo iría hasta su trono,
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
expondría ante Él mi causa, llenaría mi boca de argumentos,
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
sabría con cuáles palabras me replica, y entendería lo que me dice.
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
¿Contendería conmigo con la grandeza de su fuerza? No, más bien me atendería.
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
Allí el justo podría razonar con Él, y yo quedaría libre para siempre de mi Juez.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
Pero si voy hacia el oriente, no está allí. Y si voy al occidente, tampoco lo percibo.
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
Si muestra su poder en el norte, no lo veré, al sur se esconde y no lo veo.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
Sin embargo, Él conoce el camino por donde voy. Que me pruebe, y saldré como oro.
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
Mis pies siguieron fielmente sus huellas. Guardé su camino sin apartarme.
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
No retrocedí del mandato de sus labios, y atesoré las Palabras de su boca más que mi ración necesaria.
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
Pero Él es único. ¿Quién podrá disuadirlo? Él hace lo que desea.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
Él ejecutará lo que decretó para mí, y muchas otras cosas como ésta están en Él.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
Por lo cual me perturba su Presencia. Al pensarlo, me aterrorizo de Él.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
Porque ʼElohim hizo desmayar mi corazón. ʼEL-Shadday me aterrorizó.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
Pues no fui cortado de la presencia de la tenebrosidad, y Él no escondió mi semblante de la profunda oscuridad.