< Ayuba 23 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Job contestó:
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
“De todos modos, mis quejas hoy siguen siendo amargas. A pesar de mis gemidos, me sigue castigando.
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
Si supiera dónde puedo encontrarlo para ir a donde se sienta a juzgar.
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
Allí expondría mi caso ante él y presentaría todos mis argumentos en su totalidad.
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
Descubriría cómo me respondería y aprendería lo que tiene que decirme.
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
¿Lucharía contra mí usando su poderosa fuerza? No, prestaría atención a lo que tengo que decir.
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
Allí una buena persona podría razonar con él, y yo sería absuelto para siempre por mi juez.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
Si voy al este, él no está; si voy al oeste, no lo encuentro.
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
Si está trabajando en el norte, no lo distingo; si va al sur, no lo veo.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
“Sin embargo, él siempre sabe a dónde voy. Cuando me haya probado, saldré brillante como el oro.
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
Me he mantenido al paso con él; he seguido su camino sin desviarme.
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
No he descuidado sus mandatos, porque valoro más lo que me ha ordenado que el alimento que como cada día.
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
“Pero Dios es inmutable: ¿quién puede desviarlo de sus propósitos? Él hace todo lo que quiere hacer.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
Así que terminará lo que ha planeado para mí, y tiene muchos planes para mí.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
Por eso me aterra encontrarme con él; cuando pienso en él tiemblo de miedo.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
Dios me ha hecho desfallecer; el Todopoderoso me ha hecho morir de miedo.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
Sin embargo, sigo aquí a pesar de la oscuridad, aunque no pueda ver a través de la oscuridad total”.

< Ayuba 23 >