< Ayuba 23 >
1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Porém Jó respondeu, dizendo:
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
Até hoje minha queixa é uma amargura; a mão [de Deus] sobre mim é mais pesada que meu gemido.
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
Ah se eu soubesse como poderia achá-lo! [Então] eu me chegaria até seu trono.
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
Apresentaria minha causa diante dele, e encheria minha boca de argumentos.
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
Eu saberia as palavras que ele me responderia, e entenderia o que me diria.
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
Por acaso ele brigaria comigo com seu grande poder? Não, pelo contrário, ele me daria atenção.
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
Ali o íntegro pleitearia com ele, e eu me livraria para sempre de meu Juiz.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
Eis que se eu for ao oriente, ele não está ali; [se for] ao ocidente, e não o percebo;
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
Se ao norte ele opera, eu não [o] vejo; se ele se esconde ao sul, não [o] enxergo.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
Porém ele conhece meu caminho: Provar-me-á, e sairei como ouro.
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
Meus pés seguiram seus passos; guardei seu caminho, e não me desviei.
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
Nunca retirei [de mim] o preceito de seus lábios, e guardei as palavras de sua boca mais que minha porção [de comida].
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
Porém se ele está decidido, quem poderá o desviar? O que sua alma quiser, isso fará.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
Pois ele cumprirá o que está determinado para mim; ele [ainda] tem muitas coisas como estas consigo.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
Por isso eu me perturbo em sua presença. Quando considero [isto], tenho medo dele.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
Deus enfraqueceu meu coração; o Todo-Poderoso tem me perturbado.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
Pois não estou destruído por causa das trevas, nem por causa da escuridão que encobriu meu rosto.