< Ayuba 23 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
پس ایوب در جواب گفت:۱
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
«امروز نیز شکایت من تلخ است، وضرب من از ناله من سنگینتر.۲
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
کاش می‌دانستم که او را کجا یابم، تا آنکه نزد کرسی او بیایم.۳
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
آنگاه دعوی خود را به حضور وی ترتیب می‌دادم، ودهان خود را از حجت‌ها پر می‌ساختم.۴
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
سخنانی را که در جواب من می‌گفت می‌دانستم، و آنچه راکه به من می‌گفت می‌فهمیدم.۵
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
آیا به عظمت قوت خود با من مخاصمه می‌نمود؟ حاشا! بلکه به من التفات می‌کرد.۶
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
آنگاه مرد راست با اومحاجه می‌نمود و از داور خود تا به ابد نجات می‌یافتم.۷
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
اینک به طرف مشرق می‌روم و اویافت نمی شود و به طرف مغرب و او را نمی بینم.۸
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
به طرف شمال جایی که او عمل می‌کند، و او رامشاهده نمی کنم. و او خود را به طرف جنوب می‌پوشاند و او را نمی بینم،۹
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
زیرا او طریقی راکه می‌روم می‌داند و چون مرا می‌آزماید، مثل طلابیرون می‌آیم.۱۰
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
پایم اثر اقدام او را گرفته است وطریق او را نگاه داشته، از آن تجاوز نمی کنم.۱۱
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
از فرمان لبهای وی برنگشتم و سخنان دهان اورا زیاده از رزق خود ذخیره کردم.۱۲
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
لیکن اوواحد است و کیست که او را برگرداند؟ و آنچه دل او می‌خواهد، به عمل می‌آورد.۱۳
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
زیرا آنچه را که بر من مقدر شده است بجا می‌آورد، و چیزهای بسیار مثل این نزد وی است.۱۴
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
از این جهت ازحضور او هراسان هستم، و چون تفکر می‌نمایم از او می‌ترسم،۱۵
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
زیرا خدا دل مرا ضعیف کرده است، و قادرمطلق مرا هراسان گردانیده.۱۶
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
چونکه پیش از تاریکی منقطع نشدم، و ظلمت غلیظ را از نزد من نپوشانید.۱۷

< Ayuba 23 >