< Ayuba 23 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
욥이 대답하여 가로되
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
내가 오늘도 혹독히 원망하니 받는 재앙이 탄식보다 중함이니라
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
내가 어찌하면 하나님 발견할 곳을 알꼬 그리하면 그 보좌 앞에 나아가서
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
그 앞에서 호소하며 변백할 말을 입에 채우고
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
내게 대답하시는 말씀을 내가 알고 내게 이르시는 것을 내가 깨달으리라
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
그가 큰 권능을 가지시고 나로 더불어 다투실까 아니라 도리어 내 말을 들으시리라
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
거기서는 정직자가 그와 변론할 수 있은즉 내가 심판자에게서 영영히 벗어나리라
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
그런데 내가 앞으로 가도 그가 아니 계시고 뒤로 가도 보이지 아니하며
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
그가 왼편에서 일하시나 내가 만날 수 없고 그가 오른편으로 돌이키시나 뵈올 수 없구나
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
나의 가는 길을 오직 그가 아시나니 그가 나를 단련하신 후에는 내가 정금 같이 나오리라
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
내 발이 그의 걸음을 바로 따랐으며 내가 그의 길을 지켜 치우치지 아니하였고
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
내가 그의 입술의 명령을 어기지 아니하고 일정한 음식보다 그 입의 말씀을 귀히 여겼구나
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
그는 뜻이 일정하시니 누가 능히 돌이킬까 그 마음에 하고자 하시는 것이면 그것을 행하시나니
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
그런즉 내게 작정하신 것을 이루실 것이라 이런 일이 그에게 많이 있느니라
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
그러므로 내가 그의 앞에서 떨며 이를 생각하고 그를 두려워하는구나
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
하나님이 나로 낙심케 하시며 전능자가 나로 두렵게 하시나니
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
이는 어두움으로 나를 끊지 아니하셨고 흑암으로 내 얼굴을 가리우지 아니하셨음이니라

< Ayuba 23 >