< Ayuba 23 >
1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Da antwortete Hiob und sprach:
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
Auch heute noch ist meine Klage bitter; seine Hand preßt mir schwere Seufzer aus!
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
O daß ich wüßte, wo ich Ihn fände! Ich würde zu seinem Throne gehen.
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
Ich würde ihm die Streitfrage vorlegen und meinen Mund mit Beweisen füllen;
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
ich möchte wissen, was er mir antworten, und gerne sehen, was er zu mir sagen würde.
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
Würde er heftig mit mir streiten? Nein, er würde mich gewiß anhören.
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
Da würde der Redliche bei ihm Recht finden, und ich würde auf ewig frei ausgehen von meinem Richter.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
Wenn ich aber schon nach Osten gehe, so ist er nirgends; wende ich mich nach Westen, so werde ich seiner nicht gewahr;
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
begibt er sich nach Norden, so erspähe ich ihn nicht, verbirgt er sich im Süden, so kann ich ihn nicht sehen.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
Er aber kennt meinen Weg; er prüfe mich, so werde ich wie Gold hervorgehen!
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
Mein Fuß hat seinen Pfad innegehalten; seinen Weg habe ich bewahrt, ich bog nicht davon ab;
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
vom Gebote seiner Lippen wich ich nicht; in meinem Busen bewahrte ich die Reden seiner Lippen.
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
Doch Er bleibt sich gleich, und wer will ihn davon abbringen? Was er will, das tut er.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
Er vollführt, was mir bestimmt ist, und dergleichen hat er viel im Sinn.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
Darum schrecke ich zurück vor ihm, und wenn ich daran denke, so fürchte ich mich davor.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
Ja, Gott hat mein Herz verzagt gemacht, und der Allmächtige hat mich erschreckt.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
Daß ich [aber] nicht vergehe vor dem Anblick der Finsternis, hat er vor meinem Angesicht das Dunkel verdeckt.