< Ayuba 23 >
1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Hiob antwortete und sprach:
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
Meine Rede bleibt noch betrübt; meine Macht ist schwach über meinem Seufzen.
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
Ach daß ich wüßte, wie ich ihn finden und zu seinem Stuhl kommen möchte
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
und das Recht vor ihm sollte vorlegen und den Mund voll Verantwortung fassen
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
und erfahren die Reden, die er mir antworten, und vernehmen, was er mir sagen würde!
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
Will er mit großer Macht mit mir rechten? Er stelle sich nicht so gegen mich,
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
sondern lege mir's gleich vor, so will ich mein Recht wohl gewinnen.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
Aber ich gehe nun stracks vor mich, so ist er nicht da; gehe ich zurück, so spüre ich ihn nicht;
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
ist er zur Linken, so schaue ich ihn nicht; verbirgt er sich zur Rechten, so sehe ich ihn nicht.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
Er aber kennt meinen Weg wohl. Er versuche mich, so will ich erfunden werden wie das Gold.
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
Denn ich setze meinen Fuß auf seine Bahn und halte seinen Weg und weiche nicht ab
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
und trete nicht von dem Gebot seiner Lippen und bewahre die Rede seines Mundes mehr denn mein eigen Gesetz.
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
Doch er ist einig; wer will ihm wehren? Und er macht's wie er will.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
Denn er wird vollführen, was mir bestimmt ist, und hat noch viel dergleichen im Sinne.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
Darum erschrecke ich vor ihm; und wenn ich's bedenke, so fürchte ich mich vor ihm.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
Gott hat mein Herz blöde gemacht, und der Allmächtige hat mich erschreckt.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
Denn die Finsternis macht kein Ende mit mir, und das Dunkel will vor mir nicht verdeckt werden.