< Ayuba 23 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Et Job prit la parole, et dit:
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
Maintenant encore ma plainte est une révolte, et pourtant ma main comprime mes soupirs.
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
Oh! si je savais où le trouver, j'irais jusqu'à son trône,
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
J'exposerais ma cause devant lui, et je remplirais ma bouche de preuves;
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
Je saurais ce qu'il me répondrait, et je comprendrais ce qu'il me dirait.
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
Contesterait-il avec moi dans la grandeur de sa force? Non, seulement il ferait attention à moi.
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
Ce serait alors un juste qui raisonnerait avec lui, et je serais absous pour toujours par mon juge.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
Voici, si je vais à l'Orient, il n'y est pas; si je vais à l'Occident, je ne le découvre pas.
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
Est-il occupé au Nord, je ne le vois pas. Se cache-t-il au Midi, je ne l'aperçois pas.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
Il sait la voie que j'ai suivie; qu'il m'éprouve, j'en sortirai comme l'or.
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
Mon pied s'est attaché à ses pas, j'ai gardé sa voie, et je ne m'en suis pas détourné.
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
Je ne me suis point écarté du commandement de ses lèvres, j'ai tenu aux paroles de sa bouche plus qu'à ma provision ordinaire.
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
Mais il n'a qu'une pensée; qui l'en fera revenir? Ce que son âme désire, il le fait.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
Il achèvera ce qu'il a décidé de moi, et il a dans l'esprit bien d'autres choses pareilles à celle-ci.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
C'est pourquoi sa présence m'épouvante; quand j'y pense, j'ai peur de lui.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
Dieu a amolli mon cœur, et le Tout-Puissant m'a épouvanté.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
Car je n'ai pas été retranché avant l'arrivée des ténèbres, et il n'a pas éloigné de ma face l'obscurité.

< Ayuba 23 >