< Ayuba 23 >
1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Alors Job prit la parole et dit:
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
Oui, aujourd’hui ma plainte est amère, et pourtant ma main retient mes soupirs.
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
Oh! Qui me donnera de savoir où le trouver, d’arriver jusqu’à son trône!
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
Je plaiderais ma cause devant lui, et je remplirais ma bouche d’arguments.
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
Je saurais les raisons qu’il peut m’opposer, je verrais ce qu’il peut avoir à me dire.
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
M’opposerait-il la grandeur de sa puissance? Ne jetterait-il pas au moins les yeux sur moi?
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
Alors l’innocent discuterait avec lui, et je m’en irais absous pour toujours par mon juge.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
Mais si je vais à l’orient, il n’y est pas; à l’occident, je ne l’aperçois pas.
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
Est-il occupé au septentrion, je ne le vois pas; se cache-t-il au midi, je ne puis le découvrir.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
Cependant il connaît les sentiers où je marche; qu’il m’examine, je sortirai pur comme l’or.
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
Mon pied a toujours foulé ses traces; je me suis tenu dans sa voie sans dévier.
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
Je ne me suis pas écarté des préceptes de ses lèvres; j’ai fait plier ma volonté aux paroles de sa bouche.
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
Mais il a une pensée: qui l’en fera revenir? Ce qu’il désire, il l’exécute.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
Il accomplira donc ce qu’il a décrété à mon sujet, et de pareils desseins, il en a beaucoup.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
Voilà pourquoi je me trouble en sa présence; quand j’y pense, j’ai peur de lui.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
Dieu fait fondre mon cœur; le Tout-Puissant me remplit d’effroi.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
Car ce ne sont pas les ténèbres qui me consument, ni l’obscurité dont ma face est voilée.