< Ayuba 23 >
1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Then Job answered, and said:
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
Now also my words are in bitterness, and the hand of my scourge is more grievous than my mourning.
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
Who will grant me that I might know and find him, and come even to his throne?
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
I would set judgment before him, and would fill my mouth with complaints.
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
That I might know the words that he would answer me, and understand what he would say to me.
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
I would not that he should contend with me with much strength, nor overwhelm me with the weight of his greatness.
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
Let him propose equity against me, and let my judgment come to victory.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
But if I go to the east, he appeareth not; if to the west, I shall not understand him.
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
If to the left hand, what shall I do? I shall not take hold on him: if I turn myself to the right hand, I shall not see him.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
But he knoweth my way, and has tried me as gold that passeth through the fire:
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
My foot hath followed his steps, I have kept his way, and have not declined from it.
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
I have not departed from the commandments of his lips, and the words of his mouth I have hid in my bosom.
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
For he is alone, and no man can turn away his thought: and whatsoever is soul hath desired, that hath he done.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
And when he shall have fulfilled his will in me, many other like things are also at hand with him.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
And therefore I am troubled at his presence, and when I consider him I am made pensive with fear.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
God hath softened my heart, and the Almighty hath troubled me.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
For I have not perished because of the darkness that hangs over me, neither hath the mist covered my face.