< Ayuba 23 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
And Job made answer and said,
2 “Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
Even today my outcry is bitter; his hand is hard on my sorrow.
3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
If only I had knowledge of where he might be seen, so that I might come even to his seat!
4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
I would put my cause in order before him, and my mouth would be full of arguments.
5 Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
I would see what his answers would be, and have knowledge of what he would say to me.
6 Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
Would he make use of his great power to overcome me? No, but he would give attention to me.
7 Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
There an upright man might put his cause before him; and I would be free for ever from my judge.
8 “Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
See, I go forward, but he is not there; and back, but I do not see him;
9 Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
I am looking for him on the left hand, but there is no sign of him; and turning to the right, I am not able to see him.
10 Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
For he has knowledge of the way I take; after I have been tested I will come out like gold.
11 Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
My feet have gone in his steps; I have kept in his way, without turning to one side or to the other.
12 Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
I have never gone against the orders of his lips; the words of his mouth have been stored up in my heart.
13 “Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
But his purpose is fixed and there is no changing it; and he gives effect to the desire of his soul.
14 Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
For what has been ordered for me by him will be gone through to the end: and his mind is full of such designs.
15 Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
For this cause I am in fear before him, my thoughts of him overcome me.
16 Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
For God has made my heart feeble, and my mind is troubled before the Ruler of all.
17 Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
For I am overcome by the dark, and by the black night which is covering my face.

< Ayuba 23 >