< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Then Job responded by saying:
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
I beseech you to hear my words and to do penance.
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Permit me, and I will speak, and afterwards, if you see fit, you can laugh at my words.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
Is my dispute against man, so that I would have no reason to be discouraged?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Listen to me and be astonished, and place a finger over your mouth.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
As for me, when I think it over, I am afraid, and trembling convulses my body.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
Why then do the impious live, having been lifted up and strengthened with riches?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
They see their offspring continue before them: a commotion of close relatives and of children’s children in their sight.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Their houses have been secure and peaceable, and there is no staff of God over them.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Their cattle have conceived and have not miscarried; their cow has given birth and is not deprived of her newborn.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
Their little ones go out like a flock, and their children jump around playfully.
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
They take up the timbrel and the lyre, and they rejoice at the sound of the organ.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
Their days are prolonged in wealth, yet, in an instant, they descend into hell. (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
Who has said to God, “Depart from us, for we do not want the knowledge of your ways.
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
Who is the Almighty that we should serve him? And how is it helpful to us if we pray to him?”
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
It is true that their good things are not in their power. May the counsel of the impious be far from me!
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
How often will the lamp of the wicked be extinguished, and a deluge overtake them, and how often will he distribute the afflictions of his wrath?
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
They will be like chaff before the face of the wind, and like ashes that the whirlwind scatters.
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
God will preserve the grief of the father for his sons, and, when he repays, then he will understand.
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
His eyes will see his own destruction, and he will drink from the wrath of the Almighty.
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
For what does he care what happens to his house after him, or if the number of its months are reduced by half?
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
Can anyone teach holy knowledge to God, who judges the exalted?
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
This one dies strong and healthy, rich and happy.
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
His gut is full of fat and his bones are moistened with marrow.
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
In truth, another dies in bitterness of soul, without any resources.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
And yet they will sleep together in the dust, and worms will cover them.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Surely, I know your thoughts and your sinful judgments against me.
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
For you say, “Where is the house of the ruler, and where are the tabernacles of the impious?”
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
Ask any passerby whom you wish, and you will realize that he understands these same things:
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
that the evil-doer is reserved for the day of destruction, and he will be led to the day of wrath.
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Who will reprove his way to his face, and who will repay him for what he has done?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
He will be led to the tomb, and he will remain awake in the chaos of the dead.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
He has been found acceptable to the banks of the River of Lamentation, and he will draw any man towards him, and there are countless before him.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
Therefore, how long will you console me in vain, when your answer is shown to be repugnant to truth?

< Ayuba 21 >