< Ayuba 16 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Então Job respondeu,
2 “Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
“Já ouvi muitas coisas assim. Vocês são todos uns miseráveis confortadores!
3 Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
As palavras vãs terão um fim? Ou o que o provoca que você responda?
4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
Eu também poderia falar como você faz. Se sua alma estivesse no lugar da minha alma, Eu poderia unir palavras contra você, e abanar minha cabeça para você,
5 Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
mas eu o fortaleceria com minha boca. O consolo de meus lábios o aliviaria.
6 “Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
“Embora eu fale, meu luto não diminuiu. Apesar de eu me abster, o que me alivia?
7 Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
Mas agora, Deus, você certamente me desgastou. Vocês deixaram toda a minha empresa desolada.
8 Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
Você me encolheu. Isto é uma testemunha contra mim. Minha magreza se levanta contra mim. Ele testemunha na minha cara.
9 Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
Ele me rasgou em sua fúria e me perseguiu. Ele rangeu em cima de mim com seus dentes. Meu adversário aguça seus olhos sobre mim.
10 Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
Eles me falharam com sua boca. Eles me bateram na bochecha de forma reprovadora. Eles se reúnem contra mim.
11 Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
Deus me entrega aos ímpios, e me lança nas mãos dos ímpios.
12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
Eu estava à vontade, e ele me separou. Sim, ele me pegou pelo pescoço, e me despedaçou. Ele também me preparou para sua meta.
13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
Seus arqueiros me cercam. Ele divide meus rins, e não poupa. Ele derrama a minha bílis no chão.
14 Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
Ele me rompe com a brecha na brecha. Ele corre para mim como um gigante.
15 “Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
Cosi saco em minha pele, e empurraram meu chifre para o pó.
16 Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
Meu rosto está vermelho de lágrimas. A escuridão profunda está sobre minhas pálpebras,
17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
embora não haja violência em minhas mãos, e minha oração é pura.
18 “Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
“Terra, não cubra meu sangue. Que meu choro não tenha lugar para descansar.
19 Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
Mesmo agora, eis que minha testemunha está no céu. Aquele que garante para mim está no alto.
20 Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
Meus amigos zombam de mim. Meus olhos derramam lágrimas a Deus,
21 a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
que ele manteria o direito de um homem com Deus, de um filho do homem com seu vizinho!
22 “Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.
Para quando tiverem chegado alguns anos, Seguirei o caminho de não retorno.

< Ayuba 16 >