< Irmiya 7 >

1 Maganar da ta zo wa Irmiya ke nan daga Ubangiji.
The word that has been to Jeremiah from YHWH, saying,
2 “Ka tsaya a ƙofar gidan Ubangiji, a can kuwa ka yi shelar wannan saƙo. “‘Ku ji maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi don yin sujada ga Ubangiji.
“Stand in the gate of the house of YHWH, and you have proclaimed this word there, and have said, Hear a word of YHWH, all you of Judah, who are coming in at these gates, to bow before YHWH.”
3 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allahna Isra’ila, yana cewa ku gyara hanyoyinku da ayyukanku, zan kuwa bar ku ku zauna a wannan wuri.
Thus said YHWH of Hosts, God of Israel: “Amend your ways, and your doings, And I cause you to dwell in this place.
4 Kada ku dogara ga maganganun nan na ruɗarwa cewa, “Wannan shi ne haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji!”
Do not trust for yourselves To the words of falsehood, saying, The temple of YHWH! The temple of YHWH! These [are] the temple of YHWH!
5 In dai kuka canja hanyoyinku da ayyukanku kuma kuna aikata adalci da junanku,
For if you thoroughly amend your ways and your doings, If you thoroughly do judgment Between a man and his neighbor,
6 in ba ku zalunci baƙo, maraya ko gwauruwa ba kuma in ba ku zub da jinin marar laifi a wannan wuri ba, in kuma ba ku bi waɗansu alloli da za su cuce ku ba,
You do not oppress sojourner, fatherless, and widow, And innocent blood is not shed in this place, And [you] do not walk after other gods, for evil to yourselves,
7 to, zan bar ku ku zauna a wannan wuri, a ƙasar da na ba kakanninku har abada abadin.
Then I have caused you to dwell in this place, In the land that I gave to your fathers, From age even to age.
8 Amma ga shi, kuna dogara ga maganganu na ruɗami marasa amfani.
Behold, you are trusting for yourselves On the words of falsehood, so as not to profit.
9 “‘Za ku yi sata da kisa, ku yi zina da rantsuwar ƙarya, kuna ƙone turare wa Ba’al kuna kuma bin waɗansu allolin da ba ku sani ba,
Stealing, murdering, and committing adultery, And swearing to falsehood, and giving incense to Ba‘al, And going after other gods whom you did not know.
10 sa’an nan ku zo ku tsaya a gabana a wannan gida, wanda ake kira da Sunana, kuna cewa, “An cece mu,” mun dace mu aikata waɗannan abubuwa banƙyama?
And you have come in and stood before Me, In this house on which My Name is called, And have said, We have been delivered, In order to do all these abominations.
11 Wannan gidan da ake kira da Sunana ya zama kogon’yan fashi ne a gare ku? Amma ina kallo! In ji Ubangiji.
Has this house, On which My Name is called, Been a den of burglars in your eyes? Even I, behold, have seen,” A declaration of YHWH.
12 “‘Yanzu ku fita zuwa Shilo inda na fara maishe shi wurin zama don Sunana, ku ga abin da na yi masa saboda muguntar mutanen Isra’ila.
“But go now to My place that [is] in Shiloh, Where I caused My Name to dwell at first, And see that which I have done to it, For the wickedess of My people Israel.
13 Yayinda kuke yin dukan waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji, na yi muku magana sau da sau, amma ba ku ji ba; na kira ku, amma ba ku amsa ba.
And now, because of your doing all these works,” A declaration of YHWH, “And I speak to you, rising early and speaking, And you have not listened, And I call you, and you have not answered,
14 Saboda haka, abin da na yi wa Shilo shi ne yanzu zan yi wa gidan da ake kira da Sunana, haikalin da kuka dogara a kai, wurin da na ba ku da kuma kakanninku.
I also have done to the house on which My Name is called, In which you are trusting, And to the place that I gave to you, and to your fathers, As I have done to Shiloh.
15 Zan kore ku daga gabana, kamar yadda na yi ga dukan’yan’uwanku, mutanen Efraim.’
And I have cast you from before My face, As I have cast out all your brothers, The whole seed of Ephraim.
16 “Saboda haka kada ka yi addu’a don wannan mutane ko ka yi wani kuka ko roƙo dominsu, gama ba zan ji ka ba.
And you do not pray for this people, Nor lift up crying and prayer for them, Nor intercede with Me, for I do not hear you.
17 Ba ka gani abin da suke yi a biranen Yahuda da kuma a titunan Urushalima?
Are you not seeing what they are doing In cities of Judah, and in streets of Jerusalem?
18 Yara sukan tara itace, iyaye suka hura wuta, mata kuma sukan kwaɓa kullu don su yi wa Sarauniyar Sama waina. Sukan miƙa hadayun sha ga waɗansu alloli don su tsokane ni in yi fushi.
The sons are gathering wood, And the fathers are causing the fire to burn, And the women are kneading dough, To make cakes to the queen of the heavens, And to pour out drink-offerings to other gods, So as to provoke Me to anger.
19 Amma ni ne suke tsokana? In ji Ubangiji Ashe, ba kansu ne suke cuta, suna kunyata kansu ba?
Are they provoking Me to anger?” A declaration of YHWH, “Is it not themselves, For the shame of their own faces?”
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa fushina da hasalata za su kwarara a wannan wuri, a kan mutum da dabba, a kan itatuwan fili da a kan amfanin gona, za su yi ta kuna, ba kuwa za a kashe ba.
Therefore, thus said Lord YHWH: “Behold, My anger and My fury is poured out on this place, On man, and beast, and on tree of the field, And on fruit of the ground, And it has burned, and it is not quenched.”
21 “‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa ci gaba, ku ƙara hadayun ƙonawarku da sauran sadakoki ku kuma yi ta cin naman!
Thus said YHWH of Hosts, God of Israel: “Add your burnt-offerings to your sacrifices and eat flesh.
22 Gama sa’ad da na fitar da kakanninku daga Masar na kuma yi musu magana, ban ba su dokoki kawai game da hadayun ƙonawa da sadakoki ba,
For I did not speak with your fathers, Nor did I command them in the day of My bringing them out of the land of Egypt, Concerning the matters of burnt-offering and sacrifice,
23 amma na ba su wannan umarni cewa ku yi mini biyayya, zan kuwa zama Allahnku ku kuma ku zama mutanena. Ku yi tafiya cikin dukan hanyoyin da na umarce ku, don ku zauna lafiya.
But this thing I commanded them, saying, Listen to My voice, And I have been to you for God, And you are to Me for a people, And have walked in all the way that I command you, So that it is well for you.
24 Amma ba su saurara ba, ba su kuwa kula ba; a maimako, suka bi shawarar kansu da ta taurare muguwar zukatansu. Su ja da baya a maimakon yin gaba.
And they have not listened, nor inclined their ear, And they walk in the counsels, [And] in the stubbornness, of their evil hearts, And are backward and not forward.
25 Daga lokacin da kakanninku suka bar Masar har yă zuwa yau, kullum na yi ta aikan bayina annabawa.
Even from the day when your fathers Went out of the land of Egypt until this day, I send all My servants the prophets to you, Daily rising early and sending,
26 Amma ba su saurare ni ba, ba su kula ba. Sai suka taurare zukatansu suka aikata mugun abu fiye da na kakanninsu.’
And they have not listened to Me, Nor inclined their ear—and they harden their neck, They have done evil above their fathers.
27 “Sa’ad da ka faɗa musu wannan duka, ba za su saurare ka ba; sa’ad da ka kira su, ba za su amsa ba.
And you have spoken all these words to them, And they do not listen to you, And you have called to them, And they do not answer you.
28 Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Wannan ce al’ummar da ba tă yi biyayya ga Ubangiji Allahnta ba, ba kuwa ta karɓi gyara ba. Gaskiya ta ƙare; ta ɓace gaba ɗaya daga leɓunansu.
And you have said to them: This [is] the nation that has not listened, To the voice of its God YHWH, Nor have they accepted instruction, Steadfastness has perished, Indeed, it has been cut off from their mouth.
29 “‘Ku aske gashin kanku ku zubar; ku yi makoki a filayen tuddai, gama Ubangiji ya ƙi’yan zamanin nan ya kuma rabu da su saboda fushin da suka ba shi.
Cut off your crown, and cast [it] away, And lift up lamentation on high places, For YHWH has rejected, And He leaves the generation of His wrath.
30 “‘Mutanen Yahuda sun yi mugunta a gabana, in ji Ubangiji. Sun kafa gumakansu masu banƙyama a gidan da ake kira da Sunana suka ƙazantar da shi.
For the sons of Judah Have done evil in My eyes,” A declaration of YHWH, “They have set their abominations in the house On which My Name is called—to defile it,
31 Sun gida masujadan Tofet a Kwarin Ben Hinnom don miƙa’ya’yansu maza da mata a wuta, abin da ban yi umarni ba, ba kuwa yi tunaninsa ba.
And have built the high places of Tophet, That [are] in the Valley of the Son of Hinnom, To burn their sons and their daughters with fire, Which I did not command, Nor did it come up on My heart.
32 Saboda haka ku yi hankali, kwanaki suna zuwa in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara kira wurin Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma Kwarin Kisa, gama za su binne matattu a Tofet sai har ba sauran wuri.
Therefore, behold, days are coming,” A declaration of YHWH, “And it is no longer said, The Tophet, And, Valley of the Son of Hinnom, But, Valley of the Slaughter, And they have buried in Tophet—without place.
33 Sa’an nan gawawwakin wannan mutane za su zama abinci ga tsuntsayen sama da kuma namun jeji, ba za a kuwa sami wani da zai kore su ba.
And the carcass of this people has been for food To a bird of the heavens, and to a beast of the earth, And there is none troubling.
34 Zan kawo ƙarshen muryar murna da farin ciki da muryar amarya da ango a garuruwan Yahuda da kuma a titunan Urushalima, gama ƙasar za tă zama kufai.
And I have caused to cease from cities of Judah, And from streets of Jerusalem, The voice of joy, and the voice of gladness, Voice of bridegroom, and voice of bride, For the land becomes a desolation!”

< Irmiya 7 >