< Makoki 1 >

1 Yanzu birnin ya zama babu kowa a ciki, birnin da a dā yake cike da mutane! Yanzu birnin ya zama kamar gwauruwa, wadda a dā babba ce ita a cikin ƙasashe! Ita da take sarauniya a cikin larduna yanzu ta zama baiwa.
[ALEPH-BET] How she has sat alone, The city abounding with people! She has been as a widow, The mighty among nations! Princes among provinces, She has become tributary!
2 Tana yin kuka mai zafi da dare, hawaye na gangara a kan kumatunta. A cikin masoyanta duka babu wanda ya yi mata ta’aziyya. Duk abokanta sun yashe ta; sun zama abokan gābanta.
She weeps severely in the night, And her tear [is] on her cheeks, There is no comforter for her out of all her lovers, All her friends dealt treacherously by her, They have been to her for enemies.
3 Bayan wahala da baƙin ciki, Yahuda ta tafi bauta. Ta zauna a cikin ƙasashe, ba tă samu wurin hutawa ba. Duk masu fafararta sun same ta sa’ad da take cikin matuƙar ɓacin rai.
Removed has Judah because of affliction, And because of the abundance of her service; She has dwelt among nations, She has not found rest, All her pursuers have overtaken her between the straits.
4 Hanyoyin zuwa Sihiyona suna makoki, gama ba wanda ya zo bikin da ta shirya. Ba kowa a hanyoyin shiganta. Firistocinta suna gurnani,’yan matana kuma suna wahala, kuma tana cikin shan wahala ƙwarai.
The ways of Zion are mourning, Without any coming at the appointed time, All her gates are desolate, her priests sigh, Her virgins are afflicted—and she has bitterness.
5 Maƙiyanta sun zama shugabanninta; Abokan gābanta suna da kwanciyar rai. Ubangiji ya kawo mata ɓacin rai domin yawan zunubanta.’Ya’yanta sun tafi bauta, a ƙarƙashin maƙiyanta.
Her adversaries have become chief, Her enemies have been at ease, For YHWH has afflicted her, For the abundance of her transgressions, Her infants have gone captive before the adversary.
6 Diyar Sihiyona ba ta da sauran daraja.’Ya’yan sarakunanta sun zama kamar bareyi waɗanda suka rasa wurin kiwo; cikin rashin ƙarfi suka guje wa masu fafararsu.
And all her honor goes out from the daughter of Zion, Her princes have been as harts—They have not found pasture, And they go powerless before a pursuer.
7 A cikin kwanakin da take shan wahala take kuma yawo Urushalima ta tuna da dukan dukiyar da take da ita a kwanakin dā can. Sa’ad da mutanenta suka faɗa cikin hannun abokan gābanta, ba wanda ya taimake ta. Maƙiyanta suka dube ta suka yi mata dariya don hallakar da ta auko mata.
Jerusalem has remembered [In] the days of her affliction and her mournings, all her desirable things that were from the days of old, In the falling of her people into the hand of an adversary, And she has no helper; Adversaries have seen her, They have laughed at her cessation.
8 Urushalima ta yi zunubi ƙwarai saboda haka ta zama marar tsarki. Dukan masu martaba ta sun raina ta, gama sun ga tsiraicinta; ita ma da kanta tana nishi da ƙyar ta kuma juya baya.
A sin has Jerusalem sinned, Therefore she has become impure, All who honored her have esteemed her lightly, For they have seen her nakedness, Indeed, she herself has sighed and turns backward.
9 Ƙazantarta ta manne wa rigunanta; ba tă kula da nan gaba ba, fāɗuwarta kuwa babban abu ne; babu wanda zai yi mata ta’aziyya. “Duba, ya Ubangiji, ka ga wahalata, gama maƙiyi ya yi nasara.”
Her uncleanness [is] in her skirts, She has not remembered her latter end, And she comes down wonderfully, There is no comforter for her. See, O YHWH, my affliction, For an enemy has exerted himself.
10 Maƙiya ya kwashe dukiyarta duka; ta ga mutanen da ba su san Allah ba sun shiga wuri mai tsarkinta waɗanda ka hana su shiga taron jama’arka.
His hand has spread out an adversary On all her desirable things, For she has seen—Nations have entered her sanctuary, Concerning which You commanded, “They do not come into the assembly to you.”
11 Dukan mutanenta suna nishi da ƙyar suna neman burodi; sun sayar da dukiyarsu don su samu abinci don kada su mutu da yunwa. “Ubangiji, ka duba ka gani, gama an yashe ni.”
All her people are sighing—seeking bread, They have given their desirable things For food to refresh the body; See, O YHWH, and behold attentively, For I have been lightly esteemed.
12 “Ko wannan ba wani abu ba ne a wurinku, dukanku masu wucewa? Ku duba ku gani. Ko akwai wata wahala kamar irin wadda nake sha, wadda Ubangiji ya auko mini a cikin zafin fushinsa?
[Is it] nothing to you, all you passing by the way? Look attentively, and see, If there is any pain like my pain, That He is rolling to me? Whom YHWH has afflicted In the day of the fierceness of His anger.
13 “Daga sama ya aiko da wuta, ya aiko ta cikin ƙasusuwana. Ya shimfiɗa raga a ƙafafuna ya juyo da ni. Ya bar ni ni kaɗai, sumamme dukan yini.
From above He has sent fire into my bone, And it subdues it, He has spread a net for my feet, He has turned me backward, He has made me desolate—all the day sick.
14 “Ya ɗaura zunubaina a wuyana; aka naɗe su a hannuwansa. Aka rataye su a wuyana Ubangiji ya kwashe ƙarfina. Ya bashe ni ga waɗanda suka fi ni ƙarfi.
Bound has been the yoke of my transgressions by His hand, They are wrapped together, They have gone up on my neck, He has caused my power to stumble, The Lord has given me into hands, I am not able to rise.
15 “Ubangiji ya ƙi duk mayaƙan da suke tare da ni; ya sa wata runduna ta tayar mini ta kuma tattake samarina. Ubangiji ya tattake budurwa Diyar Yahuda kamar’ya’yan inabi a wurin matsewa.
The Lord has trodden down all my mighty ones in my midst, He proclaimed an appointed time against me, To destroy my young men, The Lord has trodden a winepress, To the virgin daughter of Judah.
16 “Dalilin da ya sa nake kuka ke nan idanuna kuma suna ta zubar da hawaye. Babu wani a kusa da zai yi mini ta’aziyya, ba wanda zai sabunta ruhuna.’Ya’yana sun zama fakirai domin maƙiyina ya yi nasara.”
For these I am weeping, My eye, my eye, is running down with waters, For a comforter has been far from me, Refreshing my soul, My sons have been desolate, For mighty has been an enemy.
17 Sihiyona ta miƙa hannunta, amma ba wani da zai yi mata ta’aziyya. Ubangiji ya umarta cewa maƙwabtansa za su zama maƙiyansa; Urushalima ta zama abar ƙyama a cikinsu.
Zion has spread forth her hands, There is no comforter for her, YHWH has charged concerning Jacob, His neighbors [are] his adversaries, Jerusalem has become impure among them.
18 “Ubangiji mai adalci ne, duk da haka na yi tawaye da umarninsa. Ku saurara, jama’a duka; ku dubi wahalar da nake sha. Samarina da’yan matana duka sun tafi bauta.
YHWH is righteous, For I have provoked His mouth. Now hear, all you peoples, and see my pain, My virgins and my young men have gone into captivity.
19 “Na kira abokaina amma sun yashe ni. Firistocina da dattawana sun hallaka a cikin birnin yayinda suke neman abinci don kada su mutu da yunwa.
I called for my lovers, they have deceived me, My priests and my elderly have expired in the city; When they have sought food for themselves, Then they give back their soul.
20 “Duba, Ubangiji, ka ga ƙuncin da nake ciki! Ina shan azaba a raina, ba ni da kwanciyar rai a cikin zuciyata, domin na yi tawaye sosai. A waje takobi na kisa; a ciki kuma akwai mutuwa.
See, O YHWH, for distress [is] to me, My bowels have been troubled, My heart has been turned in my midst, For I have greatly provoked, From outside the sword has bereaved, In the house [it is] as death.
21 “Mutane suna ji ina nishi da ƙyar, amma ba wanda zai yi mini ta’aziyya. Dukan maƙiyana sun ji wahalar da nake ciki; suna farin ciki da abin da ka yi. Ka kawo ranan nan da ka sanar domin su ma su zama kamar ni.
They have heard that I have sighed, There is no comforter for me, All my enemies have heard of my calamity, They have rejoiced that You have done [it], You have brought in the day You have called, And they are like to me.
22 “Bari ka ga muguntarsu duka; ka yi musu yadda ka yi mini domin dukan zunubansu. Nishina da yawa kuma zuciyata ta gaji.”
All their evil comes in before You, And one is doing to them as You have done to me, For all my transgressions, For many [are] my sighs, and my heart [is] sick!

< Makoki 1 >