< Irmiya 49 >

1 Game da Ammonawa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Isra’ila ba shi da’ya’ya maza ne? Ba shi da magāda ne? To, me ya sa Molek ya mallaki Gad? Me ya sa mutanensa suka zama a garuruwansa?
Aux fils d’Ammon, voici ce que dit le Seigneur: Est-ce qu’Israël n’a point d’enfants? ou n’a-t-il point d’héritiers? Pourquoi donc Melchom s’est-il emparé de Gad comme de son héritage, et son peuple a-t-il établi son habitation dans ses villes?
2 Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi kirarin yaƙi a kan Rabba ta Ammonawa; zai zama tarin juji, za a sa wuta a ƙauyukan da suke kewayenta. Sa’an nan Isra’ila zai kori waɗanda suka kore shi,” in ji Ubangiji.
C’est pourquoi, voilà que des jours viennent, dit le Seigneur, et je ferai entendre sur Rabbath des fils d’Ammon le frémissement d’un combat; et elle sera réduite par sa destruction en un monceau de pierres; et ses filles seront consumées par le feu. Israël possédera ceux qui le possédaient, dit le Seigneur
3 “Ki yi kuka, ya Heshbon, gama an hallaka Ai! Ku tā da murya ku yi kuka, ya mazaunan Rabba! Ku sa tufafin makoki; ku ruga nan da can a cikin katanga, gama Molek zai tafi bauta, tare da firistocinsa da kuma fadawansa.
Hurle, Hésébon, parce que Haï a été ravagée; criez, filles de Rabbath; ceignez-vous de cilices; pleurez, et allez autour des haies, parce que Melchom sera emmené en exil, et ses prêtres et ses princes en même temps.
4 Me ya sa kuke taƙama da kwarurukanku, taƙama da kwarurukanku masu amfani? Ya ke diya marar aminci, kin dogara a wadatarki kika kuma ce, ‘Wa zai iya fāɗa mini?’
Pourquoi te glorifies-tu dans tes vallées? ta vallée s’est écoulée; fille délicate, qui te confiais en tes trésors, et disais: Qui viendra vers moi?
5 Zan kawo razana a kanki daga waɗanda suke kewaye da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Za a kore kowannenku, babu wani da zai tattara masu gudun hijira.
Voilà que j’amènerai sur toi la terreur, dit le Seigneur, Dieu des armées, la terreur de tous ceux qui t’environnent; vous serez dispersés les uns après les autres hors de votre présence, et il n’y aura personne qui rassemblera les fuyards.
6 “Duk da haka, daga baya, zan maido da wadatar Ammonawa,” in ji Ubangiji.
Et après cela, je ferai revenir les captifs des fils d’Ammon, dit le Seigneur.
7 Game da Edom. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Babu sauran hikima a Teman ne? Shawara ta ɓace daga masu basira ne? Hikimarsu ta ruɓe ne?
À l’Idumée. Voici ce que dit le Seigneur des armées: Est-ce qu’il n’y a plus de sagesse dans Théman? Le conseil les a abandonnés, leur sagesse est devenue inutile.
8 Ku juya ku gudu, ku ɓuya a cikin kogwanni masu zurfi, ku da kuke zama a Dedan, gama zan kawo masifa a kan Isuwa a lokacin da zan hukunta shi.
Fuyez, et tournez le dos, descendez dans le gouffre, habitants de Dédan, parce que j’ai amené la ruine sur Esaü, le temps de sa visite.
9 In masu tsinkar’ya’yan inabi suka zo maka, ba za su rage’ya’yan inabi kaɗan ba? In ɓarayi suka zo da dare, ba za su sata abin da kawai suke bukata ba?
Si des vendangeurs étaient venus sur toi, ils t’auraient laissé une grappe; si des voleurs pendant la nuit, ils auraient emporté seulement ce qui leur aurait suffi.
10 Amma zan washe Isuwa sarai; zan bubbuɗe wuraren ɓuyarsa, don kada yă ɓoye kansa.’Ya’yansa, danginsa da maƙwabtansa za su hallaka, ba kuwa zai ƙara kasancewa ba.
Mais moi, j’ai découvert Esaü, j’ai révélé ce qu’il tenait caché, et il ne pourra plus être secret; sa race a été désolée, ainsi que ses frères et ses voisins; et il ne sera plus.
11 Ka bar marayunka; zan tsare ransu. Gwaurayenka kuma za su dogara a gare ni.”
Laisse tes pupilles; mais je les ferai vivre; et tes veuves en moi espéreront.
12 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In waɗanda ba su dace su sha kwaf ɗin ba suka sha shi, me ya sa za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, sai ka sha shi.
Car voici ce que dit le Seigneur: Voilà que ceux qui n’avaient pas été jugés comme devant boire le calice, le buvant, le boiront; et toi, tu seras laissé comme innocent? Tu ne seras pas regardé comme innocent; mais buvant tu boiras.
13 Na rantse da kaina,” in ji Ubangiji, “cewa Bozra za tă zama kufai da kuma abin tsoro, abin dariya da abin la’ana; kuma dukan garuruwanta za su kasance kufai har abada.”
Parce que j’ai juré par moi-même, dit le Seigneur, que Bosra deviendra une solitude, et un opprobre, et un désert, et une malédiction; et toutes ses cités deviendront des solitudes éternelles.
14 Na ji saƙo daga Ubangiji cewa; an aiki jakada zuwa ga al’ummai ya ce, “Ku tattara kanku don ku fāɗa mata! Ku tashi don yaƙi!”
J’ai entendu une nouvelle venant du Seigneur, et un messager a été envoyé vers les nations: Rassemblez-vous et venez contre elle; et levons-nous pour le combat.
15 “Yanzu zan mai da kai ƙanƙani a cikin al’ummai abin reni a cikin mutane.
Car voilà que je t’ai rendu petit parmi les nations, méprisable entre les hommes.
16 Tsoron da ka sa ake ji da kuma girman kan zuciyarka ya ruɗe ka, kai da kake zama a kogon dutse, kai da kake kan tudu. Ko da yake ka gina wa kanka sheƙa can bisa kamar na gaggafa, daga can zan sauko da kai ƙasa,” in ji Ubangiji.
Ton arrogance t’a trompé, ainsi que l’orgueil de ton cœur; toi qui habites dans des cavernes de pierres et qui t’efforces d’occuper le haut d’une colline; quand tu aurais élevé ton nid comme l’aigle, je t’arracherais de là, dit le Seigneur.
17 “Edom za tă zama abin tsoro; dukan wanda ya wuce zai giggice ya yi tsaki saboda dukan mikinta.
Et l’Idumée sera déserte; car quiconque passera au milieu d’elle sera frappée de stupeur et sifflera sur ses plaies.
18 Kamar yadda aka tumɓuke Sodom da Gomorra, tare da garuruwan da suke maƙwabtaka da su,” in ji Ubangiji, “haka ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
Comme Sodome a été renversée, ainsi que Gomorrhe et ses voisines, dit le Seigneur; un homme n’y habitera pas, et le fils d’un homme n’y séjournera pas.
19 “Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai kyau, zan kori Edom daga ƙasarta nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa don wannan? Wane ne yake kama da ni kuma wa zai kalubalance ni? Kuma wane makiyayi ne zai yi gāba da ni?”
Voilà que, comme un lion, il montera de l’orgueil du Jourdain vers une beauté puissante; parce que soudain je le ferai courir vers elle; et quel est l’élu que je préposerai sur elle? Car qui est semblable à moi? qui tiendra contre moi? et quel est le pasteur qui résistera à mon visage?
20 Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Edom, abin da ya nufa wa waɗanda suke zama a Teman. Za a ja ƙanana na garken tumaki a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
Écoutez à cause de cela le dessein que le Seigneur a formé contre Edom, et les pensées qu’il a méditées contre les habitants de Théman; il a dit: Je jure, si les petits du troupeau ne les chassent pas, et s’ils ne détruisent pas avec eux leur habitation.
21 Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza; za a kuma ji muryar kukansu a Jan Teku.
À la voix de leur ruine la terre a été agitée; la clameur de leur voix sur la mer Rouge a été entendue.
22 Duba! Gaggafa tana firiya tana kuma saukowa, tana buɗe fikafikanta a bisa Bozra. A wannan rana zukatan jarumawan Edom za su zama kamar macen da take naƙuda.
Et comme l’aigle il remontera et il s’envolera; et il étendra ses ailes sur Bosra; et le cœur des forts de l’Idumée sera en ce jour-là comme le cœur d’une femme en travail.
23 Game da Damaskus. “Hamat da Arfad sun giggice, gama sun ji mummunar labari. Suna damuwa, sun damu kamar tekun da baya hutu.
À Damas. Emath a été couvert de confusion, ainsi que Arphad, parce qu’elles ont entendu une nouvelle très mauvaise; elles ont été troublées comme sur la mer; par inquiétude elle n’a pu trouver de repos.
24 Damaskus ta karai ta juya don ta gudu tsoro kuma ya kama ta; wahala da zafi sun kama ta, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Damas a perdu courage, elle a été mise en fuite; la frayeur s’est emparée d’elle; l’angoisse et les douleurs l’ont saisie comme une femme en travail.
25 Me ya sa ba a tafi aka bar sanannen birnin nan ba, birnin da nake jin daɗi?
Comment ont-ils abandonné la cité renommée, la ville de l’allégresse?
26 Tabbatacce, samarinta za su fāɗi a tituna; dukan sojojinta za su yi shiru a wannan rana,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Pour cela ses jeunes hommes tomberont sur ses places, et tous les hommes de guerre se tairont en ce jour-là, dit le Seigneur des armées.
27 “Zan cinna wa katangar Damaskus wuta; za tă ci kagaran Ben-Hadad.”
Et j’allumerai un feu sur le mur de Damas, et il dévorera les remparts de Bénadad.
28 Game da Kedar da mulkokin Hazor, waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fāɗa wa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tashi, ku fāɗa wa Kedar ku kuma hallaka mutanen Gabas.
À Cédar, et aux royaumes d’Asor, qu’a détruits Nabuchodonosor, roi de Babylone. Voici ce que dit le Seigneur: Levez-vous, et montez vers Cédar, et ravagez les fils de l’Orient.
29 Za a ƙwace tentunansu da garkunansu; za a tafi da mafakanta tare da dukan kayayyakinsu da raƙumansu. Mutane za su yi musu ihu, ‘Razana ko’ina!’
Ils prendront leurs tabernacles et leurs troupeaux; ils prendront pour eux leurs pavillons, et leurs vases, et leurs chameaux, et ils appelleront sur eux la frayeur de toutes parts.
30 “Ku yi maza ku gudu! Ku zauna a kogo masu zurfi, ku da kuke zama a Hazor,” in ji Ubangiji. “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya shirya muku maƙarƙashiya; ya ƙulla maƙarƙashiya a kanku.
Fuyez, allez précipitamment, tenez-vous dans des antres, vous qui habitez Asor, dit le Seigneur; car Nabuchodonosor, roi de Babylone, a formé un dessein contre vous, et il a médité contre vous des pensées.
31 “Ku tashi ku kuma fāɗa wa al’umma da sauƙi wadda take zama da ƙarfin hali,” in ji Ubangiji, “al’ummar da ba ta da ƙofofi ko ƙyamare; mutanenta suna zama su kaɗai.
Levez-vous tous ensemble, et montez vers une nation tranquille, et qui habite en assurance, dit le Seigneur: ils n’ont pas de portes, ni de verrous: ils habitent seuls.
32 Za a washe raƙumansu, garkunansu mai girma za su zama ganima. Zan watsar da waɗanda suke a wurare masu nesa a ko’ina zan kuma kawo musu masifa a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
Et leurs chameaux seront au pillage; et la multitude de leurs troupeaux en proie; je les disperserai a tout vent, eux dont la chevelure est coupée; et de tous leurs confins j’amènerai la mort sur eux, dit le Seigneur.
33 “Hazor za tă zama mazaunin diloli, kufai har abada. Ba wanda zai zauna a can; ba wanda zai zauna a cikinta.”
Et Asor deviendra la demeure des dragons et un désert jusqu’à jamais; un homme n’y habitera pas, et le fils d’un homme n’y séjournera pas.
34 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Elam, a farkon mulkin Zedekiya sarkin Yahuda.
Parole du Seigneur qui fut adressée à Jérémie, le prophète, contre Elam au commencement du règne de Sédécias, roi de Juda, disant:
35 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi, zan karye ƙarfin Elam, zaunannen ƙarfinsu.
Voici ce que dit le Seigneur des armées: Voilà que moi je briserai l’arc d’Elam et toute leur force.
36 Zan kawo a kan Elam a kusurwoyi huɗu daga kusurwoyi huɗu na duniya; zan watsar da su zuwa kusurwoyi huɗu, kuma ba al’ummar da masu gudun hijirar Elam ba za su kai ba.
Et j’amènerai sur Elam quatre vents, des quatre plages du ciel; je les disperserai vers tous ces vents, et il n’y aura pas de nation à laquelle ne parviennent les fugitifs d’Elam.
37 Zan ragargaza Elam a gaban maƙiyansu, a gaban waɗanda suke neman ransu; zan kawo masifa a kansu, da zafin fushina,” in ji Ubangiji. “Zan runtume su da takobi sai na kawo ƙarshensu.
Je ferai trembler Elam devant ses ennemis et en la présence de ceux qui cherchent leur âme; et j’amènerai sur eux un malheur, la colère de ma fureur, dit le Seigneur, et j’enverrai après eux le glaive, jusqu’à ce que je les aie consumés.
38 Zan sa kursiyina a Elam in kuma hallaka sarkinta da fadawanta,” in ji Ubangiji.
Et je poserai mon trône dans Elam, j’en exterminerai les rois et les princes, dit le Seigneur.
39 “Duk da haka zan maido da wadatar Elam a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji.
Et dans les derniers jours, je ferai revenir les captifs d’Elam, dit le Seigneur.

< Irmiya 49 >