< Irmiya 48 >

1 Game da Mowab. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Kaito ga Nebo, gama za tă lalace. Kiriyatayim za su kunyata a kuma kame ta; katagar za tă sha kunya ta kuma wargaje.
À Moab, voici ce que dit le Seigneur des armées, Dieu d’Israël: Malheur à Nabo, parce qu’elle a été dévastée et couverte de confusion; Cariathaïm a été prise; la forte a été couverte de confusion, et elle a tremblé,
2 Ba za a ƙara yabi Mowab ba; a Heshbon mutane za su shirya mata maƙarƙashiya. ‘Zo, mu tafi mu kawo ƙarshe ga wannan al’umma.’ Ke kuma, ya Madmen za ki yi shiru; takobi zai fafare ki.
Il n’y a plus d’exultation dans Moab contre Hésébon; ses ennemis ont conspiré. Venez, et perdons-la entièrement comme nation; ainsi tu garderas un silence absolu, et le glaive te suivra.
3 Saurari kuka daga Horonayim, kukan risɓewa mai girma da hallaka.
Voix de clameur qui s’élève d’Oronaïm: dévastation et grande destruction.
4 Za a karye Mowab; ƙanananta za su yi kuka.
Moab est brisée, annoncez un cri à ses petits enfants.
5 Sun haura hanyar zuwa Luhit, suna kuka mai zafi yayinda suke tafiya; a hanyar da ta gangara zuwa Horonayim suna kuka a kan hallakar da aka ji.
Par la montée de Luith, gémissant, elle montera en pleur, parce qu’à la descente d’Oronaïm les ennemis ont entendu un hurlement de destruction:
6 Ku gudu! Ku gudu don tserar da ranku; ku zama kamar kurmi a hamada.
Fuyez, sauvez vos âmes; et vous serez comme des bruyères dans le désert.
7 Da yake kun dogara ga ayyukanku da arzikinku, ku ma za a kwashe ku bayi, Kemosh zai tafi bauta, tare da firistocinsa da fadawansa.
Parce que tu as eu confiance dans tes fortifications et dans tes trésors, toi aussi tu seras prise; et Chamos émigrera, et ses prêtres et ses princes en même temps.
8 Mai hallakarwa zai aukar wa kowane gari, kuma ba wani garin da zai kuɓuta. Kwari zai lalace tudu kuma ya hallaka, domin Ubangiji ya faɗa.
Et viendra un spoliateur dans toutes les villes, et nulle ville ne sera sauvée; et les vallées périront, et les campagnes seront ravagées, parce que l’a dit le Seigneur.
9 Ku sa gishiri a kan Mowab, gama za tă zama kango; garuruwanta za su zama kufai, ba mazauna a cikinsu.
Donnez une fleur à Moab, parce qu’elle sortira florissante, et ses cités seront désertes et inhabitables.
10 “La’ananne ne shi wanda yake sake a yin aikin Ubangiji! La’ananne ne wanda ya janye takobinsa daga zub da jini!
Maudit celui qui fait l’œuvre du Seigneur frauduleusement; et maudit celui qui empêche son glaive de verser le sang.
11 “Mowab ta kasance cikin kwanciyar rai tun ƙuruciyarta, kamar ruwan inabin da aka bari lis, ba a juya daga tulu zuwa wani tulu ba ba tă tafi bauta ba. Saboda haka tana da ɗanɗanonta, kuma ƙanshinta bai canja ba.
Moab dès sa jeunesse a été fertile, et il s’est reposé sur sa lie; il n’a pas été versé d’un vase dans un autre vase, et il n’a pas émigré; c’est pour cela que son goût lui est toujours demeuré, et que son parfum n’est point changé.
12 Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan aika da mutanen da za su tuntsurar da tuluna, su kuma zubar da ita waje. Za su bar tulunan ba kome a ciki su kuma farfashe tulunanta.
À cause de cela, voici que des jours viennent, dit le Seigneur, et je lui enverrai des hommes qui disposeront et renverseront ses bouteilles, et ils le renverseront lui-même, et videront ses vases, et briseront ses bouteilles.
13 Sa’an nan Mowab za tă ji kunyar Kemosh, yadda gidan Isra’ila ya ji kunya sa’ad da suka dogara ga Betel.
Et Moab sera couvert de confusion, à cause de Chamos, comme a été couverte de confusion la maison d’Israël, à cause de Béthel en qui elle avait confiance.
14 “Yaya za ku ce, ‘Mu jarumawa ne, mutane masu ƙarfi a yaƙi?’
Comment dites-vous: Nous sommes braves, et des hommes robustes pour combattre?
15 Mowab za tă hallaka a kuma kai wa garuruwanta hari; samarinta kyawawa za su gangara cikin mayanka,” in ji Sarki, wanda sunansa Ubangiji Maɗaukaki ne.
Moab a été dévastée, ses cités ont été renversées; l’élite de ses jeunes hommes a succombé dans le carnage, dit le roi, dont le nom est le Seigneur des armées.
16 “Fāɗuwar Mowab ta yi kusa; bala’inta zai auku nan da nan.
La destruction de Moab est près d’arriver, et sa ruine accourra extrêmement vite.
17 Yi kuka saboda ita, dukanku mazaunan kewayenta, duk waɗanda suka san shahararta; ku ce, ‘Dubi yadda sandan sarauta mai iko ya karye, dubi yadda sanda mai daraja ya karye!’
Consolez-le, vous tous qui êtes autour de lui; et vous tous qui savez son nom, dites: Comment a été brisée une verge puissante, un bâton glorieux?
18 “Sauko daga darajarku ku zauna a busasshiyar ƙasa, Ya mazaunan Diyar Dibon, gama shi mai hallaka Mowab zai haura a kanku zai kuma lalace biranenku masu kagarai.
Descends de la gloire, assieds-toi dans la soif, habitante de la fille de Dibon; parce que le dévastateur de Moab monte vers toi, il a détruit tes fortifications.
19 Ku tsaya a bakin hanya ku duba, ku da kuke zama a Arower. Ku tambayi mutumin da yake gudu da macen da take tserewa, tambaye su, ‘Me ya faru?’
Tiens-toi sur la voie, et fais le guet, habitante d’Aroër; interroge celui qui s’est enfui, et à celui qui s’est sauvé, dis: Qu’est-il arrivé?
20 An kunyata Mowab, gama ta wargaje. Ku yi kuka ku kuma tā da murya! Ku yi shela kusa da Arnon cewa an hallaka Mowab.
Moab a été couvert de confusion, parce qu’il a été vaincu; hurlez et criez; annoncez sur l’Arnon que Moab a été dévastée.
21 Hukunci ya zo wa tudu, zuwa Holon, Yahza da Mefa’at,
Et le jugement du Seigneur est venu jusqu’à la terre de la plaine; sur Hélon, sur Jasa, et sur Méphaath,
22 zuwa Dibon, Nebo da Bet-Dibilatayim,
Et sur Dibon, et sur Nabo, et sur la maison de Déblathaïm,
23 zuwa Kiriyatayim, Bet-Gamul da Bet-Meyon,
Et sur Cariathaïm, et sur Bethgamul, et sur Bethmaon.
24 zuwa Keriyot da Bozra zuwa dukan garuruwan Mowab, nesa da kusa.
Et sur Carioth, et sur Bosra, et sur toutes les cités de la terre de Moab qui sont loin et qui sont près.
25 An karye ƙahon Mowab; an karye hannunta,” in ji Ubangiji.
La corne de Moab a été arrachée, et son bras a été rompu, dit le Seigneur.
26 “Ku bugar da ita domin ta tayar wa Ubangiji. Bari Mowab tă yi ta birgima a cikin amanta; bari tă zama abin dariya.
Enivrez-le, parce qu’il s’est élevé contre le Seigneur; Moab se heurtera la main en tombant dans son vomissement, et il sera un objet de dérision, lui aussi.
27 Isra’ila ma bai zama abin dariya a gare ki ba? Ba a kama shi cikin ɓarayi, har kaɗa kai na ba’a kike yi a duka sa’ad da kike magana game da shi?
Car Israël a été un objet de dérision pour toi, comme si tu l’avais trouvé parmi des voleurs; à cause donc de tes paroles que tu as dites contre lui, tu seras mené captif.
28 Ku bar garuruwanku ku zauna a cikin duwatsu, ku da kuke zama a Mowab. Ku zama kamar kurciyar da take sheƙarta a bakin kogo.
Abandonnez les cités, et habitez dans la pierre, habitants de Moab; et soyez comme la colombe qui fait son nid dans la plus haute ouverture d’un rocher.
29 “Mun ji labarin girman kan Mowab mun ji alfarma girmankanta da kumburinta girmankanta da fariyarta da renin zuciyarta.
Nous avons appris l’orgueil de Moab (il est superbe à l’excès), sa hauteur et son arrogance, et son orgueil, et la fierté de son cœur.
30 Na san alfarmanta amma a banza ne,” in ji Ubangiji, “kuma taƙamarta ba ya cimma kome.
Moi, je sais, dit le Seigneur, sa jactance, et que sa force n’y répond pas, et que ce qui n’était pas selon son pouvoir, elle s’est efforcée de le faire.
31 Saboda haka zan yi kuka a kan Mowab gama dukan Mowab zan yi kuka, Zan yi gurnani don mutanen Kir Hareset.
C’est pour cela que sur Moab je pleurerai, et que j’adresserai mes cris à Moab tout entière, et aux hommes de mur de briques qui se lamentent.
32 Zan yi kuka saboda kai, yadda Yazer ya yi kuka Ya kuringar Sibma. Rassanki sun kai har teku; sun kai har tekun Yazer. Mai hallakarwa ya fāɗo a kan’ya’yan itatuwanku da kuma inabinku da suka nuna.
Du pleur de Jazer, je te pleurerai, vigne de Sabama; tes rejetons ont passé la mer, et ils sont parvenus jusqu’à la mer de Jazer; sur ta moisson et sur ta vendange un voleur s’est précipité.
33 Farin ciki da murna su ɓace daga lambunan itatuwa da kuma gonakin Mowab. Na dakatar da malalar ruwan inabi daga wurin matsi; ba wanda zai matse su da ihun farin ciki. Ko da yake akwai sowa sowar ba ta farin ciki ba ce.
L’allégresse et l’exultation ont été enlevées au Carmel et à la terre de Moab, et j’ai emporté le vin des pressoirs; et le pressureur du raisin ne chantera plus sa chanson accoutumée.
34 “Muryar kukansu na tashi daga Heshbon zuwa Eleyale da Yahaz, daga Zowar har zuwa Horonayim da Eglat Shelishiya, gama har ruwan Nimrim ma sun bushe.
Par un cri qui a retenti depuis Hésébon jusqu’à Eléalé et jusqu’à Jasa, ils ont fait entendre leur voix de Ségor, génisse de trois ans, à Oronaïm; les eaux même de Nemrim seront très mauvaises.
35 A Mowab zan kawo ƙarshen waɗanda suke miƙa hadayu a masujadan kan tudu suna kuma ƙone turare ga allolinsu,” in ji Ubangiji.
Et j’ôterai de Moab, dit le Seigneur, et celui qui fait des oblations sur les hauteurs, et celui qui sacrifie à ses dieux.
36 “Saboda haka zuciyata na makoki don Mowab kamar busa; tana makoki kamar busa saboda mutanen Kir Hareset. Arzikin da suka samu ta ƙare.
C’est pour cela que mon cœur sur Moab retentira comme une flûte; et mon cœur sur les hommes de mur de briques donnera un son de flûte; parce qu’il a fait plus qu’il ne pouvait, c’est pour cela qu’ils ont péri.
37 An aske kowane kai aka kuma yanke kowane gemu aka kuma sa wa kowane kwankwaso rigar makoki.
Car toute tête sera chauve, et toute barbe sera rasée; à toutes les mains il y aura un lien, et sur tout dos un cilice.
38 A kan dukan rufi a Mowab da kuma a dandalin jama’a babu wani abu sai kuka gama na karye Mowab kamar tulun da babu mai so,” in ji Ubangiji.
Sur tous les toits de Moab, et dans toutes ses places, on entendra toute sorte de pleurs, parce que j’ai brisé Moab comme un vase inutile, dit le Seigneur.
39 “Duba yadda aka ragargazar ta ita! Duba yadda suke kuka! Duba yadda Mowab ta juya bayanta da kunya! Mowab ta zama abin ba’a abin tsoro ga dukan waɗanda suke kewaye da ita.”
Comment a-t-elle été vaincue, et ont-ils poussé des hurlements? comment Moab a-t-il baissé la tête et a-t-il été couvert de confusion? Et Moab sera un objet de dérision et un exemple pour tous autour de lui.
40 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ga shi! Gaggafa tana firiya zuwa ƙasa, tana shimfiɗa fikafikanta a kan Mowab.
Voici ce que dit le Seigneur: Comme l’aigle il volera, et il étendra ses ailes vers Moab.
41 Za a ci Keriyot a kuma kame kagarai. A wannan rana zukatan jarumawan Mowab za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.
Carioth a été prise, les fortifications ont été emportées; et le cœur des forts de Moab sera en ce jour-là comme le cœur d’une femme en travail.
42 Za a hallakar da Mowab a matsayin al’umma domin ta tayar wa Ubangiji.
Et Moab cessera d’être un peuple, parce que contre le Seigneur il s’est glorifié.
43 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen Mowab,” in ji Ubangiji.
L’effroi, et la fosse, et le lacs pour toi, ô habitant de Moab, dit le Seigneur.
44 “Duk wanda ya gudu daga razana zai fāɗa cikin rami, duk wanda ya haura daga rami zai fāɗa cikin tarko; gama zan kawo wa Mowab shekarar hukuncinta,” in ji Ubangiji.
Qui aura fui à la face de l’effroi tombera dans la fosse, et qui sera monté de la fosse sera pris dans le lacs; car j’amènerai sur Moab l’année de leur visite, dit le Seigneur.
45 “A ƙarƙashin Heshbon masu gudun hijira suna tsaye ba mai taimako, gama wuta ta mutu daga Heshbon, harshen wuta daga tsakiyar Sihon; ta ƙone goshin Mowab, ƙoƙon kai na’yan tayarwa masu surutu.
À l’ombre d’Hésébon se sont arrêtés ceux qui fuyaient le lacs; mais un feu est sorti d’Hésébon, et une flamme du milieu de Séhon, et elle a dévoré une partie de Moab, et le sommet des fils du tumulte.
46 Kaitonki, ya Mowab! Mutanen Kemosh sun hallaka; an kai’ya’yanki maza daurin talala’ya’yanki mata zaman bauta.
Malheur à toi, Moab! tu as péri, peuple de Chamos: tes fils ont été pris, ainsi que tes filles, pour la captivité.
47 “Duk da haka zan maido da wadatar Mowab a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji. A nan hukuncin Mowab ya ƙare.
Mais je ramènerai les captifs de Moab dans les derniers jours, dit le Seigneur. Jusqu’ici les jugements contre Moab.

< Irmiya 48 >