< Irmiya 4 >

1 “In za ka komo, ya Isra’ila, ka komo gare ni,” in ji Ubangiji. “In ka kau da gumakanka masu banƙyama daga gabana ba ka ƙara karkace ba,
Yahweh says, “You Israeli [people], come back to me! If you get rid of those detestable idols and do not turn away from me [again],
2 kuma in cikin gaskiya da adalci ka rantse, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ to al’ummai za su sami albarka ta wurinsa kuma a cikinsa za su ɗaukaka.”
and if you declare, ‘Just as surely as Yahweh lives, what he says is true,’ and if you [start to] always say what is true and act justly/fairly and righteously, then the [people in the other] nations [of the world] will request that I bless them [as I have blessed you], and they will [all come and] honor/praise me.”
3 Ga abin da Ubangiji yana ce wa mutanen Yahuda da kuma na Urushalima. “Ku nome ƙasarku kuma kada ku yi shuka cikin ƙayayyuwa.
This is what Yahweh says to the people of Jerusalem and [the other cities in] Judah: “[Prepare yourselves to receive my messages] like farmers plow up hard ground [in order that they can plant seed in it]. Just as farmers do not [waste good seed by] sowing seeds among thorny plants, [I do not want to waste my time telling you messages that you are not ready to receive].
4 Ku yi wa kanku kaciya ga Ubangiji ku yi wa zukatanku kaciya, ku mutanen Yahuda da mutanen Urushalima, in ba haka ba hasalata za tă sauko ta ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci ba wanda zai kashe ta.
Purify your inner beings and your minds for me. If you do not do that, my being angry with you [MTY] because of [all] the sins that you have committed will be like a fire that will be impossible to extinguish.”
5 “Ku yi shela a Yahuda ku kuma furta a Urushalima ku ce, ‘Ku busa ƙaho a ko’ina a ƙasar!’ Ku tā da murya da ƙarfi ku ce, ‘Ku tattaru! Bari mu gudu zuwa birane masu katanga!’
“Declare this [DOU] to [all the people in] Jerusalem and [the rest of] Judea; blow the trumpets everywhere in the land [to warn the people]. Tell them that they should flee to the cities that have high walls around them.
6 Ku tā da tuta don zuwa Sihiyona! Ku gudu ku nemi mafaka ba tare da jinkiri ba! Gama ina kawowa masifa daga arewa, mummunan hallaka kuwa.”
Shout to the people of Jerusalem, ‘Run away [now]! Do not delay, because I am about to cause you to experience a terrible disaster [DOU] that will come from the north.
7 Zaki ya fito daga ruƙuƙinsa; mai hallakarwar al’ummai ya kama hanya. Ya bar wurinsa don yă lalace ƙasarku. Garuruwanku za su zama kufai babu mazauna.
[An army] that has destroyed [many] nations will attack you [like] [MET] a lion that comes out of its den [to attack other animals]. [The soldiers of that army] have taken down their tents and they are ready to march toward your land. They will destroy your cities and leave them without any people still living in them.’
8 Saboda haka ku yafa tufafin makoki, ku yi makoki da kuka, gama fushin Ubangiji bai juye daga gare mu ba.
So, put on sackcloth/rough clothes and weep and beat your chests [to show that you are very sorry for what you have done], because Yahweh is still very angry with us.
9 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “sarki da shugabanni za su fid da zuciya, firistoci za su razana, annabawa kuma za su yi mamaki.”
Yahweh said that at the time [he punishes you], the King of Judah and [all his] officials will be very afraid. The priests and the prophets will be terrified.
10 Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka, yaya ka ruɗi mutanen nan da kuma Urushalima gaba ɗaya haka ta wurin cewa, ‘Za ku zauna lafiya,’ sa’ad da takobi yana a maƙogwaronmu.”
Then I replied, “Yahweh [my] God, you completely deceived the people by telling them that there would be peace in Jerusalem, but now [our enemies] [PRS] are ready to slaughter us with their swords!”
11 A lokacin za a faɗa wa mutanen nan da kuma Urushalima cewa, “Iska mai zafi daga tuddan hamada za tă hura zuwa wajen mutanena, amma ba don ta sheƙe ko ta rairaye; ba;
When that happens, [Yahweh] will say to the people of Jerusalem, [“A huge army will come to attack you]. They will not [be like a gentle breeze that] separates wheat from chaff. [They will be like] a very hot wind [that blows in] from the desert [MET].
12 iska mafificin ƙarfi da ta fito daga gare ni. Yanzu na zartar da hukuncina a kansu.”
[They will be like] [MET] a strong blast that I will send. Now I am declaring that I will punish/destroy you.”
13 Duba! Yana zuwa kamar gizagizai, kekunan yaƙinsa suna zuwa kamar guguwa, dawakansa sun fi gaggafa sauri. Kaiton mu! Mun shiga uku!
[Our enemies] are about to rush down on us; their chariots are like [SIM] whirlwinds. Their horses are faster than eagles. It will be terrible for us!
14 Ya Urushalima, ki wanke mugunta daga zuciyarki ki sami ceto. Har yaushe za ki zauna riƙe da mugayen tunani?
[You people of] Jerusalem [APO], purify your hearts/inner beings, in order that Yahweh will rescue you. How long will you continue to think about [doing] evil things?
15 Murya ta shela daga Dan, tana furtawa masifa daga tuddan Efraim.
From Dan [city in the far north] to the hills of Ephraim [a few miles/kilometers north of Jerusalem] messengers are proclaiming that disasters are coming.
16 “A faɗa wa al’ummai wannan, a furta wannan game Urushalima. ‘Sojoji masu ƙawanya suna zuwa daga ƙasa mai nisa, suna tā da kirarin yaƙi a kan biranen Yahuda.
Tell this to the [people in other] nations [but also] announce it in Jerusalem: [Yahweh says], “An army is coming to Jerusalem from far away; they will shout [a battle-cry] against the cities in Judah.
17 Sun kewaye ta kamar masu gadin fili, domin ta yi mini tawaye,’” in ji Ubangiji.
They will set up tents around Jerusalem like people set up temporary shelters [SIM] around a field [at harvest time]. That will happen because the people of Judah have rebelled against me.
18 “Halinki da ayyukanki sun kawo wannan a kanki. Hukuncinki ke nan. Yana da ɗaci! Ya soke ki har zuciyarki!”
You will be punished very severely; it will [be as though a sword] has stabbed your inner beings. But you are causing those things to happen to you because of the evil things that you have done.”
19 Azabana, azabana! Ina birgima cikin zafi. Azabana, azabar zuciyata! Zuciyata yana bugu a cikina, Ba zan yi shiru ba. Gama na ji karan ƙaho; na ji kirarin yaƙi.
I am extremely anguished/sad; the pain in my inner being is very severe. My heart beats wildly. But I cannot remain silent because I have heard [our enemies] blowing their trumpets to announce that the battle [against Judah will start immediately].
20 Masifa kan masifa; dukan ƙasar ta zama kufai. Cikin ɗan lokaci aka rurrushe tentuna nawa, mafakata ba zato.
Disasters will occur one after another until the whole land is ruined. Suddenly [all] our tents will be destroyed; [even] the curtains [inside the tents] will be ripped apart.
21 Har yaushe zan dubi tutar yaƙi in kuma ji karar ƙaho?
How long will this battle continue? How long will I continue to see the enemy battle flags and hear the sound of their trumpets being blown?
22 “Mutanena wawaye ne; ba su san ni ba. Su’ya’ya ne marasa azanci; ba su da fahimi. Suna da dabarar aikata mugunta; ba su san yadda za su aikata alheri ba.”
[Yahweh says], “My people are [very] foolish! They do not have a relationship with me. They are [like] [MET] stupid children who do not understand [anything]. They very cleverly do what is wrong, but they do not know how to do what is good.”
23 Na dubi duniya, na ga cewa marar siffa ce babu kome; sammai kuma, haskensu ya tafi.
[God gave me a vision in which] I saw that the earth was barren and without form. I looked at the sky, and there was no light there.
24 Na dubi duwatsu, sai na ga suna makyarkyata; dukan tuddai kuwa suna lilo.
I looked at the mountains and hills, and they shook and moved from side to side.
25 Na duba, sai na ga ba kowa; kowane tsuntsu a sarari da ya tsere.
I looked and saw that there were no [more] people, and all the birds had flown away.
26 Na duba, sai na ga ƙasa mai amfani ta zama hamada; dukan garuruwanta sun zama kufai a gaban Ubangiji, a gaban zafin fushinsa.
I looked and saw that the fields that previously were fertile had become a desert. The cities were all ruined; they had all been destroyed by Yahweh because he was extremely angry.
27 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dukan ƙasar za tă zama kufai, ko da yake ba zan hallaka ta gaba ɗaya ba.
This is what Yahweh is saying: “The entire land [of Judah] will be ruined, but I will not destroy it completely.
28 Saboda haka duniya za tă yi kuka sammai a bisa kuma za su yi duhu, domin na yi magana kuma ba zan fasa ba, na yanke shawara ba kuwa zan janye ba.”
I will do to my people what I said that I would do, and I will not change my mind. So [when that happens, it will be as though] the earth will mourn and the sky will become very dark.”
29 Da jin motsin mahayan dawakai da maharba kowane gari ya ruga da gudu. Waɗansu suka shiga kurmi; waɗansu suka hau cikin duwatsu. Dukan garuruwan sun fashe tas; babu wani da yake zama a ciki.
[When the people hear] the sound of the [enemy] army marching, [they will be terrified as] they flee from their cities. Some of them will find places to hide in the bushes, and others will run toward the mountains/hills [to escape being killed by their enemies]. All the cities [in Judah] will be abandoned; not one person will remain in them.
30 Me kike yi, ya wadda aka ragargaza? Me ya sa kika sanya mulufi kika sa kayan adon zinariya? Me ya sa kika sa wa idanunki tozali? Kin yi kwalliyarki a banza. Masoyanki sun bar ki; suna neman ranki.
So you who will surely be destroyed, [why are you doing the things that you are doing now]? Why are you wearing beautiful clothes and jewelry? Why are you putting paint around your eyes? Doing those things will not help you, because the people [in other countries that you think] love you [actually] despise you, and they will try to kill you.
31 Na ji kuka kamar na mace mai naƙuda, nishi kamar na wadda take haihuwa ɗanta na fari, kukan Diyar Sihiyona tana haki, da ƙyar take numfashi, tana miƙa hannuwanta tana cewa, “Wayyo ni kaina! Na suma; an ba da raina ga masu kisana.”
[It is as though] I already hear [the people in Jerusalem] crying very loudly, like [SIM] a woman cries when she is giving birth to her first child; she gasps for breath and pleads for someone to help her. [It is as though Jerusalem] is crying, “Something terrible is happening to me! They are about to murder me!”

< Irmiya 4 >