< Ishaya 1 >

1 Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
[I am] Isaiah, the son of Amoz. [Yahweh showed me] visions about Jerusalem and [all the other places in] Judah. He showed me these visions during the years that Uzziah, Jotham, Ahaz, and Hezekiah were kings of Judah.
2 Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
This is what Yahweh says: “All you [angels in] [APO] heaven and [all you people on] [APO] earth, listen to me! The people that I caused to exist and took care of [DOU] have rebelled against me.
3 Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
Oxen know their owners, and donkeys know who provides food for them, but my Israeli people do not know [me]; they do not realize [that I am the one who takes care of them].”
4 Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
Terrible things will happen to that sinful nation, to those people who are guilty of sinning greatly. They are a group of very evil people, who act very unjustly. They have abandoned Yahweh, the holy one of Israel; they have (abandoned/turned away from) him.
5 Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
Why do you [RHQ] continue to [do things for which] you should be punished? Why do you continue to rebel against Yahweh? [You are like] [MET] someone whose head is badly injured and whose mind is sick/corrupt.
6 Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
[It is as though] [MET] from the soles/bottoms of your feet to the [tops of your] heads nothing is healthy; there are only open wounds and cuts and sores that have not been cleaned or bandaged, and no [olive] oil has been put on them [to heal them].
7 Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
[It is as though] your country is ruined/desolate; your towns have been burned. Foreigners plunder/steal the crops in your fields while you watch; they destroy everything [that they see].
8 An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
The city of Jerusalem has [already] been abandoned, it is like [SIM] a shelter in a vineyard that has been abandoned by the watchmen; it is like [SIM] a watchman’s hut in a field of melons that has been deserted. It is a city surrounded by its enemies who are waiting to attack it.
9 Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
If the Commander of the armies of angels had not allowed a few of us [his people] to (survive/remain alive), we would have [all] been [destroyed], like [the cities of] Sodom and Gomorrah [were destroyed].
10 Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
You [leaders of Judah are as wicked as] the rulers of Sodom were, and you [other people in Jerusalem areas are as wicked as] the people in Gomorrah [were]. Listen to this message from Yahweh, [all of you]!
11 Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
He says, “You continue to bring many sacrifices to me, but I do not [RHQ] want them [because you do not worship me sincerely]! You bring me many offerings to be completely burned [on the altar], [but] I (am tired/do not want any more) of your burning all those offerings, the burning rams and the fat from fat cattle. I am not pleased with the blood of bulls and lambs and goats that [the priest] pours [against the altar].
12 Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
When you come to my temple to worship me, no one [RHQ] told you to trample on my courtyard while you perform all those rituals.
13 Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
Stop bringing to me those offerings, because they are useless [to me]; I am disgusted with the incense that [the priests burn]. And [your feasts to celebrate] the new moon [each month] and your (Sabbath [days]/days of rest) and your [other] festivals— I detest them because of the wicked things [that you do].
14 Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
I [SYN] hate [all] your celebrations of each new moon and the [other] festivals that you celebrate each year. They are [like] [MET] a heavy burden that I am tired of carrying.
15 Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
[So], when you lift up your hands when you pray [to me], I will not [even] look at you. Even if you pray [to me very] frequently, I will not listen [to you], [because it is as though] your hands are covered with the blood [of people whom you have killed].
16 Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
Cleanse your inner beings, and become [spiritually] clean! Stop your evil behavior! Stop doing things that are wrong!
17 Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
Learn to do [things that are] good! [Try to] cause people to do what is just. Help people who are (oppressed/treated cruelly). Defend orphans and widows [when people take them to court].”
18 Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
Yahweh says, “You need to think about the results of what you do. Even though [the guilt of] your sins be [as evident and as difficult to get rid of] as [SIM] red [stains on a white garment] [DOU], [I will get rid of them completely] [like someone who can make that stained garment] become as white as snow or wool [DOU].
19 In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
If you are willing to obey [me], [I will enable] you to have plenty to eat.
20 amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
But, if you turn away [from me and] rebel against me, you will be killed [by your enemies’] swords. [That will surely happen, because I, ] Yahweh, have said it.”
21 Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
“[You people of Jerusalem previously] faithfully [worshiped only] me, but now you have become like [MET] prostitutes [who are not faithful to any husband]. Previously, people there always acted justly/fairly and righteously, but now your city [is full of] murderers.
22 Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
Previously, you were [like] [MET] pure silver, but now you have become [like] [MET] the scum that is left [when silver is purified]. Previously you were [like pure] wine, but you have become [like] [MET] wine that has [a lot of] water mixed with it.
23 Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
Your leaders are rebels; they spend time with thieves. They all want to get bribes and force others to give them gifts [in order that they do good things for them]. They do not defend orphans [in court], and they do not do all they can to enable widows to get what they should receive.
24 Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
Therefore [I, ] the Commander of the armies of angels, the mighty God of Israel, say to my enemies, ‘will get revenge on you; you will not cause me any more trouble. And I will pay you back for the evil things that you did.
25 Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
I will raise my fist to strike you. I will [punish you severely] [MET], as though [MET] you were silver [and I needed to heat you very greatly to] melt you and get rid of the impurities.
26 Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
[After that happens, ] I will give you good judges like you had previously; you will have [wise] counselors like you had long ago. Then people will call your city “a city where people [act] righteously, a city where people are loyal to me.”'”
27 Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
Because the people of Jerusalem will do what is fair/just, their city will be restored; those who repent [will be saved] because of [their acting] righteously.
28 Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
But rebels and sinners will be crushed by Yahweh, and those who forsake him will disappear.
29 “Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
You will be ashamed because [you worshiped] idols under the oak trees [that you considered to be] sacred; you will be disgraced because [you worshiped idols] in the gardens where you chose [to worship them].
30 Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
You will be like [SIM] a very large tree which has withered leaves, like [SIM] a garden that [is dried up because] it has no water.
31 Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”
Those among you who are [very] strong will become [like] [MET] dry wood, and the work they do will be [like] [MET] a spark; both they and the evil things that they do will burn up completely, and no one will be able to put out the fire.

< Ishaya 1 >