< Irmiya 37 >

1 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya naɗa Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda; ya yi mulki a madadin Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim.
Zedequias, filho de Josias, reinou como rei em vez de Conias, filho de Jeoiaquim, a quem Nabucodonosor, rei da Babilônia, fez rei na terra de Judá.
2 Shi da masu yin masa hidima da mutanen ƙasar ba su kula da maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya annabi ba.
Mas nem ele, nem seus servos, nem o povo da terra escutaram as palavras de Javé, que ele falou pelo profeta Jeremias.
3 Sai sarki Zedekiya ya aiki Yehukal ɗan Shelemiya tare da firist nan Zefaniya ɗan Ma’asehiya da wannan saƙo cewa, “Ina roƙonka ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnmu saboda mu.”
O rei Zedequias enviou Jehucal, filho de Selemias, e Sofonias, filho de Maaséias, o sacerdote, ao profeta Jeremias, dizendo: “Reza agora a Javé, nosso Deus, por nós”.
4 To, fa, Irmiya ya sami’yancin kai da kawowa a cikin mutane, gama ba a riga an sa shi a kurkuku ba.
Agora Jeremias entrou e saiu entre o povo, pois eles não o haviam colocado na prisão.
5 Sojojin Fir’auna suka fita daga Masar, sa’ad da Babiloniyawa waɗanda suke ƙawanya wa Urushalima suka ji labari game da su, sai suka janye daga Urushalima.
O exército do Faraó tinha saído do Egito; e quando os caldeus que estavam sitiando Jerusalém ouviram notícias deles, eles se retiraram de Jerusalém.
6 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya annabi cewa,
Então veio a palavra de Javé ao profeta Jeremias, dizendo:
7 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aika a neme ni cewa, ‘Sojojin Fir’aunan da suka fito su taimake ka, za su koma ƙasarsu, Masar.
“Javé, o Deus de Israel, diz: “Dirás ao rei de Judá, que te enviou a mim para me inquirir: “Eis que o exército do Faraó, que saiu para ajudá-lo, voltará para o Egito em sua própria terra”.
8 Sa’an nan Babiloniyawa za su koma su yaƙi wannan birni su ci ta su kuma ƙone shi.’
Os caldeus virão novamente, e lutarão contra esta cidade. Eles a tomarão e a queimarão com fogo”.
9 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku ruɗe kanku, kuna tsammani, ‘Tabbatacce Babiloniyawa sun bar mu.’ Ba za su bari ba!
“Yahweh diz: 'Não se iludam, dizendo: “Os caldeus certamente irão partir de nós;” pois eles não irão partir.
10 Ko da a ce za ku ci dukan sojojin Babiloniyawan da suke yaƙi da ku har raunana ne kawai aka bari a tentunansu, za su fito su ƙone wannan birni.”
Pois embora vocês tivessem atingido todo o exército dos caldeus que lutam contra vocês, e só ficassem entre eles homens feridos, cada um deles se levantaria em sua tenda e queimaria esta cidade com fogo””.
11 Bayan sojojin Babiloniyawa suka janye daga Urushalima saboda sojojin Fir’auna,
Quando o exército dos caldeus se retirou de Jerusalém por medo do exército do Faraó,
12 sai Irmiya ya bar birnin don yă je yankin Benyamin ya sami rabon mallaka a cikin mutane a can.
então Jeremias saiu de Jerusalém para ir para a terra de Benjamim, para receber sua porção lá, no meio do povo.
13 Amma sa’ad da ya kai Ƙofar Benyamin, sai hafsa mai tsaro, wanda ake kira Iriya ɗan Shelemiya, ɗan Hananiya, ya kama shi ya kuma ce, “Kana gudu daga Babiloniyawa ne!”
Quando ele estava no portão de Benjamim, estava lá um capitão da guarda, cujo nome era Irijah, o filho de Selemias, filho de Hananias; e ele agarrou Jeremias, o profeta, dizendo: “Você está desertando para os caldeus”!
14 Sai Irmiya ya ce, “Ba gaskiya ba ce, ba na gudu daga Babiloniyawa.” Amma Iriya bai saurare shi ba; a maimako, ya kama Irmiya ya kawo shi wurin fadawa.
Então Jeremias disse: “Isso é falso! Eu não estou desertando para os caldeus”. Mas ele não o ouviu; então Irijah apreendeu Jeremias e o trouxe até os príncipes.
15 Suka yi fushi da Irmiya suka sa aka yi masa dūka aka kuma jefa shi cikin kurkuku a gidan Yonatan magatakarda, gama an mai da gidansa ya zama kurkuku.
Os príncipes ficaram zangados com Jeremias, e o golpearam, e o colocaram na prisão na casa de Jonathan, o escriba; pois eles tinham feito isso na prisão.
16 Aka sa Irmiya a can cikin kurkuku, inda ya kasance kwanaki masu yawa.
Quando Jeremias entrou na casa do calabouço e nas celas, e Jeremias ficou lá muitos dias,
17 Sa’an nan Sarki Zedekiya ya aika a kawo shi aka kuma kawo shi fada, inda ya tambaye shi a kaɗaice ya ce, “Akwai wata magana daga Ubangiji?” Irmiya ya amsa ya ce, “I, za a ba da kai ga sarkin Babilon.”
então Zedequias, o rei, enviou e mandou trazê-lo para fora. O rei perguntou-lhe secretamente em sua casa: “Há alguma palavra de Javé? Jeremiah disse: “Há”. Ele também disse: “Você será entregue na mão do rei da Babilônia”.
18 Sai Irmiya ya ce wa Sarki Zedekiya, “Wane laifi na yi maka ko fadawanka ko kuwa wannan mutane, da ka sa aka jefa ni cikin kurkuku?
Moreover Jeremias disse ao rei Zedequias: “Como pequei contra você, contra seus servos, ou contra este povo, que você me colocou na prisão?
19 Ina annabawanka waɗanda suka yi maka annabci suna cewa, ‘Sarkin Babilon ba zai yaƙe ka ko wannan ƙasa ba’?
Agora, onde estão teus profetas que te profetizaram, dizendo: 'O rei da Babilônia não virá contra ti, nem contra esta terra?
20 Amma yanzu, ranka yă daɗe, sarkina, ka saurara. Bari in kawo kukata a gabanka. Kada ka mai da ni gidan Yonatan magatakarda, in ba haka zan mutu a can.”
Agora, por favor, ouve, meu senhor, o rei: por favor, que minha súplica seja apresentada diante de ti, para que não me faças voltar à casa de Jonathan, o escriba, para que eu não morra lá”.
21 Sarki Zedekiya ya yi umarni a ajiye Irmiya a sansanin matsara a kuma ba shi burodi daga titin masu gashin burodi kowace rana sai duka burodi a birnin ya ƙare. Saboda haka Irmiya ya zauna a sansanin matsara.
Então Zedequias, o rei, ordenou, e eles internaram Jeremias na corte da guarda. Davam-lhe diariamente um pão fora da rua dos padeiros, até que todo o pão da cidade tivesse desaparecido. Assim, Jeremias permaneceu na corte da guarda.

< Irmiya 37 >