< Ishaya 1 >

1 Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
A visão de Isaías, filho de Amoz, que ele viu a respeito de Judá e Jerusalém, nos dias de Uzias, Jotão, Acaz e Ezequias, reis de Judá.
2 Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
Ouça, céus, e escute, terra; pois Yahweh falou: “Eu alimentei e criei crianças e eles se rebelaram contra mim.
3 Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
O boi conhece seu dono, e o burro, o berço de seu amo; mas Israel não sabe. Meu povo não considera”.
4 Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
Ah nação pecadora, um povo carregado de iniqüidade, descendência de malfeitores, crianças que lidam de forma corrupta! Eles abandonaram Yahweh. Eles desprezaram o Santo de Israel. Eles são estranhos e retrógrados.
5 Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
Por que você deveria ser mais espancado? que você se revolta mais e mais? A cabeça inteira está doente, e todo o coração desmaia.
6 Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
Desde a sola do pé até a cabeça não há nenhuma solidez nele, mas feridas, vergões e feridas abertas. Eles não foram fechados, enfaixados, nem acalmados com óleo.
7 Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
Seu país está desolado. Suas cidades são queimadas pelo fogo. Estranhos devoram sua terra em sua presença e é desolado, como derrubado por estranhos.
8 An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
A filha de Sião é deixada como um abrigo em um vinhedo, como uma cabana em um campo de melões, como uma cidade sitiada.
9 Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
Unless O Yahweh dos Exércitos deixou para nós um pequeno remanescente, teríamos sido como Sodoma. Nós teríamos sido como Gomorra.
10 Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
Ouçam a palavra de Yahweh, governantes de Sodoma! Escutem a lei de nosso Deus, povo de Gomorra!
11 Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
“Quais são a multidão de seus sacrifícios para mim?”, diz Yahweh. “Estou farto das ofertas queimadas de carneiros e a gordura dos animais alimentados. Eu não me deleito com o sangue de touros, ou de cordeiros, ou de caprinos machos.
12 Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
Quando você vier para comparecer diante de mim, quem exigiu isto em suas mãos, para pisar em meus tribunais?
13 Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
Não traga mais ofertas vãs. O incenso é uma abominação para mim. Luas novas, sábados e convocações... Eu não suporto montagens malignas.
14 Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
Minha alma odeia suas Luas Novas e suas festas designadas. Eles são um fardo para mim. Estou cansado de suportá-los.
15 Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
Quando você estender suas mãos, eu esconderei meus olhos de você. Sim, quando você faz muitas orações, eu não vou ouvir. Suas mãos estão cheias de sangue.
16 Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
Lavem-se. Limpe-se. Afaste o mal de seus atos de diante dos meus olhos. Cessar de fazer o mal.
17 Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
Aprenda a fazer bem. Buscar a justiça. Aliviar os oprimidos. Defender os órfãos de pai. Plead para a viúva”.
18 Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
“Venha agora, e vamos raciocinar juntos”, diz Yahweh: “Embora seus pecados sejam tão escarlate, eles serão tão brancos como a neve”. Embora sejam vermelhas como carmesim, devem ser como lã.
19 In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
Se você estiver disposto e obediente, você vai comer o bem da terra;
20 amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
mas se você recusar e se rebelar, você será devorado com a espada; pois a boca de Yahweh o disse”.
21 Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
Como a cidade fiel se tornou uma prostituta! Ela estava cheia de justiça. A justiça nela depositada, mas agora há assassinos.
22 Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
Sua prata se tornou escória, seu vinho misturado com água.
23 Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
Seus príncipes são rebeldes e companheiros de ladrões. Todos adoram subornos e seguem atrás de recompensas. Eles não defendem os órfãos de pai, nem a causa da viúva vem até eles.
24 Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
Portanto, o Senhor, Yahweh dos Exércitos, o Poderoso de Israel, diz: “Ah, eu terei alívio de meus adversários”, e me vingar de meus inimigos.
25 Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
Vou virar minha mão para você, purgar completamente sua escória, e lhe tirará toda a lata.
26 Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
Vou restaurar seus juízes como no início, e seus conselheiros, como no início. Em seguida, você será chamada de “A cidade da retidão”, uma cidade fiel'.
27 Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
Zion será redimida com justiça, e seus convertidos com retidão.
28 Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
Mas a destruição de transgressores e pecadores deve ser feita em conjunto, e aqueles que abandonarem Yahweh serão consumidos.
29 “Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
Pois eles terão vergonha dos carvalhos que desejaram, e você ficará confuso com os jardins que escolheu.
30 Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
Para você será como um carvalho cuja folha desbota, e como um jardim que não tem água.
31 Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”
O forte será como o tinder, e seu trabalho como uma faísca. Ambos irão queimar juntos, e ninguém os saciará”.

< Ishaya 1 >