< Irmiya 26 >

1 A farkon sarautar Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo daga wurin Ubangiji,
Soon after Jehoiakim became the king of Judah, Yahweh gave [me] this message:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka tsaya a filin gidan Ubangiji ka kuma yi magana ga dukan mutanen garuruwan Yahuda waɗanda suka zo sujada a gidan Ubangiji. Ka faɗa musu kome da na umarce ka; kada ka bar wata magana.
“This is what [I], Yahweh, am telling you: Stand in the courtyard [in front] of my temple, and speak to all [the people from] the various towns in Judah who come there to worship me. Tell them everything that I tell you; do not omit anything.
3 Wataƙila su saurara kowanne kuma ya juyo daga mugun hanyarsa. Sa’an nan in yi juyayi in kuma janye masifar da nake shirin kawo a kansu saboda muguntar da suka aikata.
[If you do tell them everything], perhaps they will pay attention, and each one of them will turn away from his evil behavior. Then I will change my mind, and not cause them to experience the disaster that I was planning to cause them to experience because of the evil things that they have done.
4 Ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, in ba ku saurare ni, ku kuma bi dokata, wadda na sa a gabanku ba,
Say to them, ‘This is what Yahweh says: I sent to you the prophets who serve me, to tell you what you should do. I sent them to you many times, but you have not paid attention to what they said. If you will not pay attention to what I say and do not obey the message that I have given to you, and if you do not pay attention to what the prophets say,
5 in kuma ba ku saurari maganganun bayina annabawa, waɗanda na aika muku sau da sau ba (ko da yake ba ku saurara ba),
6 to, sai in mai da gidan nan kamar Shilo, birnin nan kuma abin la’ana a cikin al’umman duniya.’”
I will destroy this temple like I destroyed Shiloh, [the place where the Sacred Tent was put]. And I will cause Jerusalem to be a place whose name [people in] every nation on the earth will say when they curse someone.’”
7 Firistoci, annabawa da dukan mutane suka ji Irmiya yana waɗannan maganganu a gidan Ubangiji.
[When I did what Yahweh told me to do, ] the priests, the [false] prophets, and many [other] people listened to me as I told them that message outside the temple.
8 Amma da Irmiya ya gama faɗar wa dukan mutanen abin da Ubangiji ya umarce shi ya faɗa, sai firistoci, annabawa da dukan mutane suka kama shi suka ce, “Mutuwa za ka yi!
But as soon as I finished telling them everything that Yahweh had commanded me to say, they all seized me and said, “You must be executed!
9 Me ya sa ka yi annabci da sunan Ubangiji cewa wannan gida zai zama kamar Shilo, wannan birni kuma zai zama kango da hamada?” Sai duk mutane suka tattaru kewaye da Irmiya a cikin gidan Ubangiji.
Why [RHQ] are you prophesying that this temple will be [destroyed] like Shiloh [was destroyed]? Why are you saying that this city will be destroyed, and that no one will live here [any more]? (OR, You should not be prophesying) [RHQ]” All the people surrounded me [as I stood] in [front of] the temple.
10 Da fadawan Yahuda suka ji haka, sai suka haura daga fada zuwa gidan Ubangiji suka zazzauna a wuraren zamansu a mashigin Sabuwar Ƙofar gidan Ubangiji.
When the officials of Judah heard about all this [that was happening], they rushed from the palace and sat down at the gate of the temple named The New Gate, [to judge my case].
11 Sa’an nan firistoci da annabawa suka ce wa fadawan da dukan mutane, “Mutumin nan ya cancanci hukuncin kisa gama ya yi annabci gāba da wannan birni. Ku kun ji da kunnuwanku!”
The priests and the [false] told the officials and the other people [who were there], “This man should be executed, because he has prophesied that this city [will be destroyed], and you yourselves [MTY] have heard him say that!”
12 Sai Irmiya ya ce wa dukan fadawa da kuma dukan mutane, “Ubangiji ya aiko ni in yi annabci gāba da wannan gida da wannan birni dukan abin da na faɗa.
Then I replied to the officials and the other people, saying, “Yahweh sent me to prophesy all the things that you heard me say about [what will happen to] this temple and this city.
13 Yanzu sai ku gyara hanyoyinku da kuma ayyukanku ku yi biyayya da Ubangiji Allahnku. Sa’an nan Ubangiji zai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kanku.
But if you change your behavior and stop sinning, and [start to] obey Yahweh our God, he will change his mind, and not cause you to experience the disasters that he said that he would send.
14 Game da ni dai, ina a hannuwanku; ku yi duk abin da kuka ga ya yi kyau, ya kuma dace a gare ku.
As for me, I am not able to free myself from your grasp. [So you can] do to me whatever you want to do.
15 Ku tabbata dai, cewa in kuka kashe ni, za ku jawo wa kanku alhakin jini marar laifi a kanku da a kan birnin nan da kuma a kan masu zama a cikinsa, gama a gaskiya Ubangiji ne ya aiko ni wurinku domin in faɗa muku dukan maganan nan a kunnuwanku.”
[But you need to] know that if you kill me, you will be killing a man [SYN] who (is innocent/has not done anything wrong). And you and everyone else in this city will be guilty, because the truth is that it was Yahweh who sent me to speak every word that you have heard me say.”
16 Sai fadawa da dukan mutane suka ce wa firistoci da annabawa. “Wannan mutum bai yi abin da ya isa hukuncin kisa ba, gama ya yi magana da sunan Ubangiji Allahnmu.”
Then the officials and the other people said to the priests and the [false] prophets, “This man does not deserve to be executed, because he has spoken to us the message [MTY] that Yahweh gave him!”
17 Waɗansu daga cikin dattawan ƙasar suka zo gaba suka ce wa dukan taron jama’a,
Then some of the elders stood up and spoke to all the people who were gathered [there].
18 “Mika mutumin Moreshet, ya yi annabci a kwanakin Hezekiya sarkin Yahuda. Ya ce wa dukan mutanen Yahuda, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “‘Za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuwa za tă zama tsibin juji, ƙwanƙolin dutsen haikali kuwa zai zama kurmi.’
They said, “([Remember/Think about) what] Micah, [the prophet] from Moresheth [town], prophesied during the years that Hezekiah was the King of Judah. He told the people of Judah this: ‘This is what the Commander of the armies of angels says: [Some day] Zion [Hill] will be plowed like fields [are plowed]; Jerusalem will become a heap of ruins. There will be a large clump/group of trees on top of the hill where the temple is now.’
19 “Hezekiya sarkin Yahuda ko kuwa wani a Yahuda ya kashe shi? Ashe, Hezekiya bai ji tsoron Ubangiji ya nemi tagomashinsa ba? Ubangiji kuwa bai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kansu ba? Muna gab da jawo wa kanmu muguwar masifa!”
But did [RHQ] King Hezekiah or anyone else in Judah kill Micah [for saying that]? No! Instead, Hezekiah revered Yahweh, and pleaded that he would (act mercifully toward/not destroy) them. So, Yahweh changed his mind about causing them to experience the terrible disaster that he said he would send. And now [if we kill Jeremiah], we are going to cause ourselves to experience a terrible disaster!”
20 (To, fa, Uriya ɗan Shemahiya daga Kiriyat Yeyarim wani mutum ne wanda ya yi annabci da sunan Ubangiji; ya yi annabci irin abu ɗaya gāba da wannan birni da wannan ƙasa yadda Irmiya ya yi.
[At that time, ] the son of Shemaiah from Kiriath-Jearim [city] was also prophesying/proclaiming messages [MTY] from Yahweh. He was predicting that the city and the rest of the land would experience the same disasters that I was predicting.
21 Da sarki Yehohiyakim da dukan fadawansa da ma’aikatansa suka ji wannan magana, sai sarki ya nemi a kashe shi. Amma Uriya ya ji wannan shiri sai ya gudu zuwa Masar don tsoro.
When King Jehoiakim and his army officers and officials heard what Uriah was saying, the king sent someone to kill Uriah. But Uriah heard about it, and became [very] afraid, and he (escaped/ran away) to Egypt.
22 Sarki Yehohiyakim ya aiki Elnatan ɗan Akbor zuwa Masar, tare da waɗansu mutane.
Then King Jehoiakim sent Elnathan the son of Acbor along with several other men to Egypt.
23 Suka dawo da Uriya daga Masar suka kawo shi wurin Sarki Yehohiyakim, wanda ya kashe shi da takobi aka kuma jefar da gawarsa a makabartar talakawa.)
They captured Uriah and took him [back to Jerusalem] to King Jehoiakim. The king then [had a soldier] kill Uriah with a sword. Then they buried his corpse in a place where poor people are buried.
24 Bugu da ƙari, Ahikam ɗan Shafan ya goyi bayan Irmiya, saboda haka ba a ba da shi ga mutane don su kashe shi ba.
However, Ahikam the son of Shaphan defended me, and persuaded the officials not to allow [MTY] the mob to murder me.

< Irmiya 26 >