< Irmiya 21 >

1 Magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji sa’ad da Sarki Zedekiya ya aiki Fashhur ɗan Malkiya da firist Zefaniya ɗan Ma’asehiya gare shi. Suka ce masa,
Detta är det ord, som af Herranom skedde till Jeremia, då Konung Zedekia sände till honom Pashur, Malchia son, och Zephanja, Maaseja Prestens son, och lät säga honom:
2 “Yanzu ka roƙi mana Ubangiji saboda Nebukadnezzar sarkin Babilon yana kawo mana yaƙi. Wataƙila Ubangiji zai yi mana waɗansu abubuwa banmamaki kamar a lokacin baya don yă janye daga gare mu.”
Fråga dock Herran för oss; ty NebucadNezar, Konungen i Babel, örligar emot oss; att Herren dock ville göra med oss efter all sin under, på det han må draga ifrån oss.
3 Amma Irmiya ya amsa musu ya ce, “Ku faɗa wa Zedekiya cewa,
Jeremia sade till dem: Detta säger till Zedekia:
4 ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yake cewa ina shirin juya kayan yaƙin da suke a hannuwanka a kanka, waɗanda kake amfani don ka yaƙi sarki Babilon da kuma Babiloniyawa waɗanda suka kewaye katangar birnin, zan kuwa tsiba kayan yaƙinka a tsakiyar birnin nan.
Så säger Herren Israels Gud: Si, jag skall vända de vapen tillbaka, som I uti edra händer hafven, der I med striden emot Konungen i Babel, och emot de Chaldeer, som eder omkring murarna belagt hafva; och skall församla dem i en hop midt i stadenom.
5 Ni da kaina zan yi yaƙi da kai da miƙaƙƙen hannu mai ƙarfi cikin fushi da hasala mai girma.
Och jag skall strida emot eder med uträckto hand, med starkom arm, med stor vrede, grymhet och obarmhertighet;
6 Zan kashe waɗanda suke zaune a wannan birni, mutane da dabbobi za su kuwa mutu da muguwar annoba.
Och skall slå inbyggarena i denna stadenom, både folk och fä, så att de skola dö i en stor pestilentie.
7 Bayan wannan, in ji Ubangiji, zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da kuma mutanen wannan birni waɗanda suka tsira daga annoba, takobi da kuma yunwa, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Zai kashe su da takobi; ba zai ji tausayinsu ko ya yi musu jinƙai ko ya yi juyayinsu ba.’
Och derefter, säger Herren, skall jag gifva Zedekia, Juda Konung, samt med hans tjenare, och folkena, som i denna stadenom af pestilentie, svärd och hunger qvarlefde äro, uti NebucadNezars händer, Konungens i Babel, och uti deras fiendars händer, och uti deras händer som efter deras lif stå, att han så skall slå dem med svärdsegg, att der ingen skonan, eller nåde, eller barmhertighet med skall vara.
8 “Bugu da ƙari, ka faɗa wa mutanen cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ga shi na sa a gabanku hanyar rai da hanyar mutuwa.
Och säg desso folkena: Så säger Herren: Si, jag sätter eder före vägen till lifvet, och vägen till döden.
9 Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba. Amma duk wanda ya fita ya miƙa kansa ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye ku zai rayu; zai kuɓutar da ransa.
Hvilken som blifver i denna stadenom, han måste dö igenom svärd, hunger och pestilentie; men den som gifver sig ut till de Chaldeer, som eder belägga, han skall blifva lefvandes, och skall behålla sitt lif, likasom ett byte.
10 Na ƙudura in yi wa wannan birni lahani ba alheri ba, in ji Ubangiji. Za a ba da shi a hannuwan sarki Babilon, zai kuwa hallaka shi da wuta.’
Ty jag hafver ställt mitt ansigte öfver denna staden till olycko, och till intet godt, säger Herren; han skall Konungenom i Babel öfvergifven varda, att han skall uppbränna honom med eld.
11 “Ban haka ma, ka faɗa wa gidan sarauta na Yahuda cewa, ‘Ku saurari maganar Ubangiji;
Och hörer Herrans ord, I af Juda Konungs huse.
12 Ya gidan Dawuda ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ku yi gaskiya kowace safiya; ku kuɓuta daga hannun mai danniya wannan da aka yi wa fashi in ba haka ba hasalata za tă sauka ta kuma ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci babu wanda zai kashe ta.
Du Davids hus, detta säger Herren: Håller domen om morgonen, och hjelper den beröfvada utu våldsverkarens hand, på det min grymhet icke skall utfara lika som en eld, och brinna så, att det ingen utsläcka kan, för edart onda väsendes skull.
13 Ina gāba da ku, mazaunan Urushalima, ku da kuke zama a bisa wannan kwari kan dutsen da yake a fili, in ji Ubangiji ku da kuke cewa, “Wa zai iya yaƙe mu? Wa zai iya shiga mafakarmu?”
Si, säger Herren: Jag säger dig, du som bor i dalenom, på bergen och på jemna markene, och säger: Ho vill öfverfalla oss, eller komma in uti vårt fäste?
14 Zan hukunta ku gwargwadon ayyukanku, in ji Ubangiji. Zan sa wuta a kurminku da za tă cinye kome da yake kewaye da ku.’”
Jag vill hemsöka eder, säger Herren, efter edra gerningars frukt; jag skall upptända en eld uti edar skog, han skall förtära allt det deromkring är.

< Irmiya 21 >