< Irmiya 20 >

1 Da firist nan Fashhur ɗan Immer, babban ma’aikaci a cikin haikalin Ubangiji, ya ji Irmiya yana annabcin waɗannan abubuwa,
Men då Pashur, Immers son, Prestens, den för en öfversta i Herrans hus satt var, hörde Jeremia prophetera dessa orden,
2 sai ya sa aka yi wa Irmiya dūka aka kuma sa shi a turu a Ƙofar Bisa na Benyamin a haikalin Ubangiji.
Slog han Propheten Jeremia, och kastade honom i fängelse, i den öfra portenom BenJamins, hvilken på Herrans huse är.
3 Kashegari, sa’ad da Fashhur ya fitar da shi daga turu, sai Irmiya ya ce masa, “Ubangiji ba zai kira ka Fashhur ba, amma ya ba ka suna Magor-Missabib.
Och då morgonen kom, tog Pashur Jeremia åter utu fängelset. Då sade Jeremia till honom: Herren kallar dig icke Pashur, utan Magor allt omkring.
4 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan maishe ka abin razana ga kanka da kuma ga dukan abokanka; da idanunka za ka gan takobin abokan gāba yana kashe su. Zan miƙa Yahuda duka ga sarkin Babilon, wanda zai kwashe su zuwa Babilon ya kuma kashe su da takobi.
Ty så säger Herren: Si, jag skall gifva dig, samt med alla dina vänner, uti en fruktan, och de skola falla genom dina fiendars svärd; det skall du se med din ögon; och jag skall öfvergifva hela Juda uti Konungens hand af Babel; han skall föra dem bort till Babel, och dräpa dem med svärd.
5 Zan ba wa abokan gābansu dukan dukiyar wannan birni dukan amfaninsa, dukan abubuwa masu daraja na sarakunan Yahuda. Za su kwashe su ganima su kai su Babilon.
Och jag skall gifva allt godset i denna staden, samt med allt hans arbete och alla klenodier, alla Juda Konungars håfvor, uti deras fiendars hand, så att de skola dem skinna, borttaga och till Babel föra.
6 Kai kuma Fashhur, da dukan waɗanda suke a gidanka za ku tafi zaman bauta a Babilon. A can za ku mutu a kuma binne ku, da kai da dukan abokanka waɗanda ka yi musu annabce-annabcen ƙarya.’”
Och du, Pashur, skall med allt ditt husfolk gå fången, och till Babel komma; der skall du dö, och begrafven varda, samt med alla dina vänner, hvilkom du lögn predikar.
7 Ya Ubangiji, ka ruɗe ni, na kuwa ruɗu; ka fi ni ƙarfi, ka kuwa yi nasara. Na zama abin dariya dukan yini; kowa yana yi mini ba’a.
Herre, du hafver dragit mig, och jag hafver mig draga låtit; du hafver varit mig för stark, och hafver vunnit; men jag är deröfver kommen till spott dagliga, och hvar man gör gäck af mig.
8 Duk sa’ad da na yi magana, nakan tā da murya ina furta hargitsi da hallaka. Haka maganar Ubangiji ta kawo mini zagi da reni dukan yini.
Ty sedan jag talat, ropat och predikat hafver om den plågan och förderfvet, är mig Herrans ord vordet till hån och spott dagliga.
9 Amma in na ce, “Ba zan ambace shi ba ba zan ƙara yin magana da sunansa ba,” sai in ji maganarsa a cikina kamar wuta, wutar da aka kulle a ƙasusuwana. Na gaji da danne ta a cikina; tabbatacce ba zan iya ba.
Då föll mig i sinnet: Jag vill intet mer tänka uppå honom, och intet mer predika i hans Namn; men i mino hjerta och minom benom vardt lika som en brinnande eld insluten, så att jag icke förmådde det lida, och var hardt när förgången.
10 Na ji mutane da yawa suna raɗa cewa, “Razana ta kowace fuska! Mu kai kararsa! Bari mu kai kararsa!” Dukan abokaina suna jira in yi tuntuɓe, suna cewa, “Mai yiwuwa a ruɗe shi; sai mu yi nasara a kansa mu ɗau fansa a kansa.”
Ty jag hörer, huru månge banna mig, och jag måste allestäds vara rädder. Anklager, vi vilje anklaga honom, säga alle mine vänner och stallbröder; om vi kunne blifva honom öfvermägtige, och komma åt honom, och hämnas öfver honom.
11 Amma Ubangiji yana tare da ni kamar babban jarumi; saboda haka masu tsananta mini za su yi tuntuɓe ba kuwa za su yi nasara ba. Za su fāɗi su kuma sha mummunar kunya; ba za a taɓa manta da rashin bangirmansu ba.
Men Herren är med mig, såsom en stark hjelte; derföre skola mine förföljare falla, och icke vinna, utan skola på stor skam komma, derföre att de så dårliga handla; evig skall den skammen vara, och skall icke förgäten varda.
12 Ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake gwada adali kana bincika zuciya duk da tunani, bari in ga sakayyarka a kansu, gama a gare ka na miƙa damuwata.
Och nu, Herre Zebaoth, du som pröfvar de rättfärdiga, och ser njurar och hjerta, låt mig se dina hämnd öfver dem; ty jag hafver befallt dig min sak.
13 Ku rera ga Ubangiji! Ku yabi Ubangiji! Ya kuɓutar da ran mabukaci daga hannuwan mugaye.
Sjunger Herranom, lofver Herran, som hjelper dens fattigas lif utu de ondas händer.
14 La’ananniya ce ranar da aka haife ni! Kada ranar da mahaifiyata ta haife ni ta zama mai albarka!
Förbannad vare den dag, der jag uti född var; den dagen vare osignad, på hvilkom min moder mig födt hafver.
15 La’ananne ne mutumin da ya kawo wa mahaifina labari, wanda ya sa shi ya yi murna cewa, “An haifa maka yaro, ɗa namiji!”
Förbannad vare den som minom fader god tidende bar, och sade: Du hafver fått en ungan son, på det han skulle glädja honom.
16 Bari mutumin ya zama kamar garuruwan da Ubangiji ya tumɓuke ba tausayi. Bari yă ji kuka da safe kururuwan yaƙi kuma da tsakar rana.
Den mannen vare såsom de städer som Herren omvände, och honom det intet ångrade; han höre ett skriande om morgonen, och om middagen ett jämrande.
17 Gama bai kashe ni a cikin ciki ba, da ma ya sa cikin mahaifiyata ya zama kabarina, cikinta ya fadada har abada.
Att du dock icke hafver dräpit mig i moderlifvena; att min moder måtte varit min graf, och hennes lif måtte evinnerliga hafvandes varit!
18 Me ya sa na ma fito daga cikin ciki in ga wahala da baƙin ciki in kuma ƙare kwanakina da kunya?
Hvi är jag dock utu moderlifvena framkommen, att jag sådana jämmer och hjertans sorg se måste, och slita mina dagar med skam?

< Irmiya 20 >