< Irmiya 19 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tafi ka sayo tulu a wurin mai ginin tukwane. Ka ɗauki waɗansu dattawan jama’a da kuma na firistoci
Ainsi a dit l'Eternel: va, et achète une bouteille de terre d'un potier, et [prends] des anciens du peuple, et des anciens des Sacrificateurs;
2 ku fita zuwa Kwarin Ben Hinnom, kusa da mashigin Ƙofar Kasko. A can ka furta maganganun da na faɗa maka,
Et sors à la vallée du fils de Hinnom, qui est auprès de l'entrée de la porte Orientale, et crie là les paroles que je te dirai.
3 ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ya sarakunan Yahuda da kuma mutanen Urushalima. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku saurara! Zan kawo masifa a wannan wuri, wanda duk ya ji, kunnuwansa za su kaɗa.
Dis donc: Rois de Juda, et vous habitants de Jérusalem, écoutez la parole de l'Eternel: ainsi a dit l'Eternel des armées, le Dieu d'Israël: voici, je m'en vais faire venir sur ce lieu-ci un mal, tel que quiconque l'entendra, les oreilles lui en tinteront.
4 Gama sun yashe ni suka kuma mai da wannan wuri ya zama na baƙin alloli; sun ƙone hadayu a cikinsa wa allolin da ko su ko kakanninsu ko sarakunan Yahuda ba su taɓa sani ba, suka kuma cika wannan wuri da jini marasa laifi.
Parce qu'ils m'ont abandonné, et qu'ils ont profané ce lieu, et y ont fait des encensements à d'autres dieux, que ni eux, ni leurs pères, ni les Rois de Juda n'ont point connus, et parce qu'ils ont rempli ce lieu du sang des innocents;
5 Suka gina masujadai na kan tudu na Ba’al don su ƙona’ya’yansu maza a cikin wuta a matsayin hadaya ga Ba’al abin da ban umarta ba, ban ambata ba, bai kuma zo mini ba.
Et qu'ils ont bâti des hauts lieux de Bahal, afin de brûler au feu leurs fils pour en faire des holocaustes à Bahal, ce que je n'ai point commandé, et dont je n'ai point parlé, et à quoi je n'ai jamais pensé;
6 Saboda haka ku lura, kwanaki suna zuwa, in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara ce da wannan wuri Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma za su ce da shi Kwarin Kisa.
A cause de cela voici, les jours viennent, dit l'Eternel, que ce lieu-ci ne sera plus appelé Topheth, ni la vallée du fils de Hinnom, mais la vallée de la tuerie.
7 “‘A wannan wuri zan lalace dabarun Yahuda da na Urushalima. Zan sa a kashe su da takobi a gaban abokan gābansu, a hannuwan waɗanda suke neman ransu, zan kuma ba da gawawwakinsu su zama abinci ga tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji.
Et j'anéantirai le conseil de Juda et de Jérusalem en ce lieu-ci, et je les ferai tomber par l'épée en la présence de leurs ennemis, et en la main de ceux qui cherchent leur vie; et je donnerai leurs corps morts à manger aux oiseaux des cieux et aux bêtes de la terre.
8 Zan ragargazar da wannan birni in mai da shi abin reni, duk wanda ya wuce zai yi mamaki ya kuma yi tsaki saboda dukan masifunsa.
Je détruirai cette ville, et je la couvrirai d'opprobre; quiconque passera près d'elle sera étonné, et lui insultera à cause de toutes ses plaies.
9 Zan sa su ci naman’ya’yansu maza da mata, za su kuma ci naman juna a lokacin damuwar ƙawanya da abokan gāban da suke neman ransu za su yi musu.’
Et je leur ferai manger la chair de leurs fils, et la chair de leurs filles; et chacun mangera la chair de son compagnon durant le siège, et dans l'extrémité où les réduiront leurs ennemis, et ceux qui cherchent leur vie.
10 “Sa’an nan ka fasa tulun yayinda waɗanda suka tafi tare da kai suna duba,
Puis tu casseras la bouteille en présence de ceux qui seront allés avec toi;
11 ka kuma ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa zan farfasa wannan al’umma da wannan birni kamar yadda aka farfasa wannan tulu mai ginin tukwane ba kuwa zai gyaru ba. Za a binne matattu a Tofet har sai ba sauran wuri.
Et tu leur diras: ainsi a dit l'Eternel des armées: je briserai ce peuple et cette ville, de même qu'on brise un vaisseau de potier, qui ne peut être soudé, et ils seront ensevelis à Topheth, parce qu'il [n'y aura] plus d'autre lieu pour [les] ensevelir.
12 Ga abin da zan yi wa wannan wuri da waɗanda suke zaune a nan, in ji Ubangiji. Zan mai da wannan birni kamar Tofet.
Je ferai ainsi à ce lieu-ci, dit l'Eternel, et à ses habitants; tellement que je réduirai cette ville au même état que Topheth;
13 Gidaje a Urushalima da waɗannan na sarakunan Yahuda za su ƙazantu kamar wannan wuri, Tofet, dukan gidajen da suke ƙone turare a kan rufi wa duk rundunan taurari suna kuma zuba hadayun sha ga sauran alloli.’”
Et les maisons de Jérusalem, et les maisons des Rois de Juda seront souillées, comme le lieu de Topheth, à cause de toutes les maisons sur les toits desquelles ils ont fait des parfums à toute l'armée des cieux, et des aspersions à d'autres dieux.
14 Sa’an nan Irmiya ya komo daga Tofet, inda Ubangiji ya aike shi don yă yi annabci, ya tsaya a filin haikalin Ubangiji ya ce wa mutane duka,
Puis Jérémie s'en vint de Topheth là où l'Eternel l'avait envoyé pour prophétiser, et il se tint debout au parvis de la maison de l'Eternel, et dit à tout le peuple:
15 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ku saurara! Zan kawo wa wannan birni da ƙauyukan da suke kewayensa kowace masifar da na furta a kansu, domin sun yi taurinkai, ba su kuwa saurari maganata ba.’”
Ainsi a dit l'Eternel des armées, le Dieu d'Israël: voici, je m'en vais faire venir sur cette ville, et sur toutes ses villes, tout le mal que j'ai prononcé contre elle, parce qu'ils ont raidi leur cou, pour ne point écouter mes paroles.

< Irmiya 19 >