< Irmiya 14 >

1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya game da fări cewa,
RAB kuraklığa ilişkin Yeremya'ya şöyle seslendi:
2 “Yahuda tana makoki biranenta suna fama; suna kuka saboda ƙasar, kuka kuma tana tasowa daga Urushalima.
“Yahuda yas tutuyor, Kentleri bitkin; Halkı karalar giymiş, yerlere oturmuş, Yeruşalim'in haykırışı yükseliyor.
3 Manyan mutane suna aika bayinsu su ɗebo ruwa a maɓulɓulai amma babu ruwa. Suka dawo da tulunansu haka nan; da kunya da kuma ƙasƙanci, da kawunansu a rufe.
Soylular uşaklarını suya gönderiyorlar. Sarnıçlara gidiyor, ama su bulamıyor, Kapları boş dönüyorlar. Aşağılanmış, utanç içinde, Başlarını örtüyorlar.
4 Ƙasa ta tsattsage saboda babu ruwan sama a ƙasar; manoma sun sha kunya suka kuma rufe kawunansu.
Ülke yağmursuz, toprak çatlamış, Irgatlar utanç içinde başlarını örtüyorlar.
5 Har barewa a kurmi ma ta gudu ta bar’ya’yan da ta haihu sababbi saboda babu ciyawa.
Kırdaki geyik bile Yeni doğmuş yavrusunu bırakıyor, Çünkü ot yok.
6 Jakan jeji suna tsaye a kan tuddai suna haki kamar diloli; idanunsu sun kāsa gani saboda rashin makiyaya.”
Yaban eşekleri çıplak tepelerde durmuş, Çakal gibi soluyorlar; Gözlerinin feri sönmüş, Çünkü otlak yok.”
7 Ko da yake zunubanmu suna ba da shaida a kanmu, Ya Ubangiji, ka yi wani abu saboda sunanka. Gama jan bayanmu ya yi yawa; mun yi maka zunubi.
Suçlarımız bize karşı tanıklık etse de, Adın uğruna bir şeyler yap, ya RAB! Pek çok döneklik ettik, Sana karşı günah işledik.
8 Ya kai, Sa Zuciyar Isra’ila, Mai Cetonsa a lokutan wahala, me ya sa kake yi kamar baƙo a ƙasar, kamar matafiyi wanda yake shirya wuri don yă kwana gari ya waye ya wuce?
Ey İsrail'in Umudu, Sıkıntı anlarındaki Kurtarıcısı! Neden ülkede bir yabancı, Ancak bir gece konaklayan yolcu gibisin?
9 Me ya sa kake yi kamar mutumin da aka far masa kwasam ba zato, kamar jarumi marar ƙarfin ceto? Kana a cikinmu, ya Ubangiji, da sunanka ake kiranmu; kada ka yashe mu!
Neden şaşırmış biri gibi, Kurtarmaya gücü yetmeyen savaşçı gibisin? Aramızdasın sen, ya RAB, Seniniz, bırakma bizi!
10 Ga abin da Ubangiji ya ce game da wannan mutane, “Suna son yawace-yawace ƙwarai; ba sa hana ƙafafunsu yawo. Saboda haka Ubangiji bai yarda da su ba; yanzu zai tuna da muguntarsu zai kuma hukunta su saboda zunubansu.”
Bu halk için RAB diyor ki, “Gezip tozmayı pek sever, Ayaklarını dolaşmaktan esirgemezler. Bu yüzden RAB onlardan hoşnut değil, Şimdi anımsayacak suçlarını, Günahları için onları cezalandıracak.”
11 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Kada ka yi addu’a domin zaman lafiyar mutanen nan.
Sonra RAB bana, “Bu halkın iyiliği için yalvarma” dedi,
12 Ko da yake suna azumi, ba zan saurari kukansu ba, ko da yake suna miƙa hadayun ƙonawa da hadayun gari, ba zan yarda da su ba. A maimako zan hallaka su da takobi, yunwa da annoba.”
“Oruç tutsalar bile feryatlarına kulak vermeyeceğim. Yakmalık sunu, tahıl sunusu sunsalar bile kabul etmeyeceğim. Tersine, kılıçla, kıtlıkla, salgın hastalıkla yok edeceğim onları.”
13 Amma na ce, “A, Ubangiji Mai Iko Duka, annabawa sun riƙa ce musu, ‘Ba za ku ga takobi ko ku yi fama da yunwa ba. A maimako, zan ba ku madawwamiyar salama.’”
Bunun üzerine, “Ah, Egemen RAB, peygamberler bu halka, ‘Kılıç yüzü görmeyecek, kıtlık çekmeyeceksiniz; burada size kalıcı esenlik sağlayacağım’ diyorlar” dedim.
14 Sai Ubangiji ya ce mini, “Annabawa suna ta annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba, ban kuma naɗa su ba, ban yi musu magana ba. Suna muku annabci wahayin ƙarya, suna muku duba marar amfani, suna bautar gumaka suna kuma bayyana tunanin kansu ne.
RAB, “Peygamberler benim adımla yalan peygamberlik ediyorlar” dedi, “Onları ne gönderdim, ne onlara buyruk verdim, ne de seslendim. Size uydurma görümlerden, falcılıktan, boş şeylerden, akıllarından geçen hayallerden söz ediyorlar.
15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce game da annabawan da suke annabci da sunana. Ban aike su ba, duk da haka suna cewa, ‘Babu takobi ko yunwar da zai taɓa wannan ƙasa.’ Waɗannan annabawa takobi da yunwa za su hallaka su.
Adımla konuşan peygamberler için ben RAB diyorum ki, onları göndermediğim halde, ‘Bu ülkede kılıç da kıtlık da olmayacak’ diyorlar. Ama kendileri de kılıçla, kıtlıkla yok olacaklar.
16 Mutanen da suke musu annabcin kuwa za a kore su zuwa titunan Urushalima saboda yunwa da kuma takobi. Babu wanda zai binne su, ko ya binne matansu, ko’ya’yansu maza da mata. Zan aukar musu da masifar da ya dace da su.
Peygamberlik ettikleri halk da kıtlık ve kılıç yüzünden Yeruşalim sokaklarına atılacak. Onları da karılarını, oğullarını, kızlarını da gömecek kimse olmayacak. Yaptıkları kötülüğü kendi başlarına getireceğim.
17 “Ka yi musu wannan magana, “‘Bari idanuna su yi ta zub da hawaye dare da rana kada su daina; saboda’yata budurwa, mutanena, sun sha wahalar babban rauni, an yi musu bugu mai ragargazawa.
“Onlara de ki, “‘Gözlerim gece gündüz Durmadan gözyaşı döksün, Çünkü erden kızım, halkım Ağır bir yara aldı, Ezici bir darbe yedi.
18 In na shiga cikin ƙasar, na ga waɗanda takobi ya kashe; in na shiga cikin birni, na ga waɗanda suke fama da yunwa. Da Annabi da firist duk sun tafi ƙasar da ba su sani ba.’”
Kıra çıksam, kılıçtan geçirilenleri, Kente girsem, kıtlıktan kırılanları görüyorum. Olup bitenden habersiz peygamberlerle kâhinlerse Ülkeyi dolaşıp duruyorlar.’”
19 Ka ƙi Yahuda ɗungum ke nan? Kana ƙyamar Sihiyona ne? Me ya sa ka buge mu don kada mu warke? Mun sa zuciya ga salama babu abin alherin da ya zo, mun sa rai ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
Yahuda'yı büsbütün mü reddettin? Siyon'dan tiksiniyor musun? Neden şifa bulmayacak kadar yaraladın bizi? Esenlik bekledik, iyilik gelmedi. Şifa umduk, yılgınlık bulduk.
20 Ya Ubangiji, mun gane da muguntarmu da kuma laifin kakanninmu; tabbatacce mun yi maka zunubi.
Yaptığımız kötülükleri, Atalarımızın suçlarını biliyoruz, ya RAB; Gerçekten sana karşı günah işledik.
21 Saboda sunanka kada ka ƙi mu; kada ka ƙasƙantar da kursiyoyinka mai ɗaukaka. Ka tuna da alkawarinka da mu kada ka tā da shi.
Adın uğruna bizi küçümseme, Görkemli tahtının hor görülmesine izin verme. Bizimle yaptığın antlaşmayı anımsa, Bozma onu.
22 Akwai wani daga cikin gumaka marasa amfani na al’ummai da ya kawo ruwan sama? Sararin sama kansu sukan yi yayyafi? A’a, kai ne, ya Ubangiji Allahnmu. Saboda haka sa zuciyarmu tana a kanka, gama kai ne kake yi wannan duka.
Ulusların değersiz putlarından herhangi biri Yağmur yağdırabilir mi? Gökler kendiliğinden Sağanak yağdırabilir mi? Bunu yalnız sen yapabilirsin, Ya RAB Tanrımız. Umudumuz sende, Çünkü bütün bunları yapan sensin.

< Irmiya 14 >