< Irmiya 14 >

1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya game da fări cewa,
After there had been no rain [in Judah] for a long time, Yahweh gave me this message:
2 “Yahuda tana makoki biranenta suna fama; suna kuka saboda ƙasar, kuka kuma tana tasowa daga Urushalima.
[The people in] Judah are very distressed; people [are sitting] on the ground and mourning; [in all of] Jerusalem people are crying loudly.
3 Manyan mutane suna aika bayinsu su ɗebo ruwa a maɓulɓulai amma babu ruwa. Suka dawo da tulunansu haka nan; da kunya da kuma ƙasƙanci, da kawunansu a rufe.
The rich people send their servants to [wells] to get water, but [all] the wells are dry. The servants return with empty pitchers; they cover their heads [because they are ashamed and humiliated/disappointed and sad].
4 Ƙasa ta tsattsage saboda babu ruwan sama a ƙasar; manoma sun sha kunya suka kuma rufe kawunansu.
The ground is extremely dry and cracked open because there has been no rain. The farmers are very worried, [so] they [also] cover their heads.
5 Har barewa a kurmi ma ta gudu ta bar’ya’yan da ta haihu sababbi saboda babu ciyawa.
Even the (does/female deer) abandon their newborn babies/fawns because there is no grass in the fields [for them to eat].
6 Jakan jeji suna tsaye a kan tuddai suna haki kamar diloli; idanunsu sun kāsa gani saboda rashin makiyaya.”
The wild donkeys stand on the barren hills, panting like [SIM] [thirsty] jackals/wolves. They become blind because there is no grass [to eat].
7 Ko da yake zunubanmu suna ba da shaida a kanmu, Ya Ubangiji, ka yi wani abu saboda sunanka. Gama jan bayanmu ya yi yawa; mun yi maka zunubi.
[The people say], “Yahweh, we have turned away from you and sinned many times, and now we know that we are being punished because of our sins, but please help us in order that everyone can see that you are very great [MTY].
8 Ya kai, Sa Zuciyar Isra’ila, Mai Cetonsa a lokutan wahala, me ya sa kake yi kamar baƙo a ƙasar, kamar matafiyi wanda yake shirya wuri don yă kwana gari ya waye ya wuce?
You are the one whom [we] Israelis confidently expect [to do good things for us] when we have [many] troubles/difficulties. So, why do you [not help us]? You act as though you are a stranger in our land, like you are someone who is staying here for only one night.
9 Me ya sa kake yi kamar mutumin da aka far masa kwasam ba zato, kamar jarumi marar ƙarfin ceto? Kana a cikinmu, ya Ubangiji, da sunanka ake kiranmu; kada ka yashe mu!
Are you also surprised [about the terrible things that are happening to us]? Why do you act like you are unable to save anyone, even though you are a strong warrior? Yahweh, you are [here] among us, and [others know that] we are your people, [so] do not abandon us!”
10 Ga abin da Ubangiji ya ce game da wannan mutane, “Suna son yawace-yawace ƙwarai; ba sa hana ƙafafunsu yawo. Saboda haka Ubangiji bai yarda da su ba; yanzu zai tuna da muguntarsu zai kuma hukunta su saboda zunubansu.”
And this is what Yahweh says to those people: “You love to wander away [from me]; you run [MTY] from one [idol] to another. Therefore, now I will no [longer] accept you, and I will punish you for your sins.”
11 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Kada ka yi addu’a domin zaman lafiyar mutanen nan.
[Then] Yahweh said to me, “Do not pray for these people [any more].
12 Ko da yake suna azumi, ba zan saurari kukansu ba, ko da yake suna miƙa hadayun ƙonawa da hadayun gari, ba zan yarda da su ba. A maimako zan hallaka su da takobi, yunwa da annoba.”
When they (fast/abstain from food in order to honor me), I will not pay any attention. When they bring [to me] their offerings [of animals] to be completely burned [on the altar] and their offerings of grain, I will not accept them. Instead, I will get rid of them by wars, by famines, and by diseases.”
13 Amma na ce, “A, Ubangiji Mai Iko Duka, annabawa sun riƙa ce musu, ‘Ba za ku ga takobi ko ku yi fama da yunwa ba. A maimako, zan ba ku madawwamiyar salama.’”
Then I replied to him, “Yahweh [my] God, [their] prophets are telling the people that they will not experience wars [MTY] or famines. They are telling the people that you will surely allow us to have peace in our land [for many years].”
14 Sai Ubangiji ya ce mini, “Annabawa suna ta annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba, ban kuma naɗa su ba, ban yi musu magana ba. Suna muku annabci wahayin ƙarya, suna muku duba marar amfani, suna bautar gumaka suna kuma bayyana tunanin kansu ne.
Yahweh replied to me, “Those prophets say that they are speaking what I tell them to say [MTY], but they are telling lies. I did not send them, [so] what they are saying is false. They say that they have received visions from me, and that they are telling things that I have revealed to them, but that is not true. They are saying foolish things that they have only thought of themselves.
15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce game da annabawan da suke annabci da sunana. Ban aike su ba, duk da haka suna cewa, ‘Babu takobi ko yunwar da zai taɓa wannan ƙasa.’ Waɗannan annabawa takobi da yunwa za su hallaka su.
So this is what I say about those prophets who are predicting what will happen, saying that I told them those things: They are saying that we Israelis will not die from wars or famines, but I did not send those prophets. And they themselves will die from wars or from famines.
16 Mutanen da suke musu annabcin kuwa za a kore su zuwa titunan Urushalima saboda yunwa da kuma takobi. Babu wanda zai binne su, ko ya binne matansu, ko’ya’yansu maza da mata. Zan aukar musu da masifar da ya dace da su.
And the people to whom they are predicting these things, they and their wives and their sons and their daughters, will [also die] from wars or from famines. [Their corpses will] be thrown into the streets of Jerusalem, and there will not be anyone to bury them. I will punish them like they deserve to be punished.
17 “Ka yi musu wannan magana, “‘Bari idanuna su yi ta zub da hawaye dare da rana kada su daina; saboda’yata budurwa, mutanena, sun sha wahalar babban rauni, an yi musu bugu mai ragargazawa.
[So, Jeremiah], tell this to them [about yourself]: ‘Day and night my eyes are full of tears. I cannot stop crying. I cry for my people, who are [very precious to me, as if they were] [MET] my daughters. I cry for them because they have been severely wounded; they have been severely crushed [DOU].
18 In na shiga cikin ƙasar, na ga waɗanda takobi ya kashe; in na shiga cikin birni, na ga waɗanda suke fama da yunwa. Da Annabi da firist duk sun tafi ƙasar da ba su sani ba.’”
If I go out into the fields, I see [corpses of] people who have been slaughtered by our enemies. If I walk along the streets of the city, I see [corpses of people who died] from hunger. The prophets and the priests travel through the land, preaching to people, but they do not know [what they are doing] (OR, [in a land] that they know nothing about).’”
19 Ka ƙi Yahuda ɗungum ke nan? Kana ƙyamar Sihiyona ne? Me ya sa ka buge mu don kada mu warke? Mun sa zuciya ga salama babu abin alherin da ya zo, mun sa rai ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
[Then I prayed this]: “[Yahweh], have you completely rejected [the people of] Judah? Do you really despise [the people of] Jerusalem [MTY]? Why have you [RHQ] wounded us very badly, with the result that we will never be healed? We hoped that we would have peace, but there was no peace. We hoped that there would be a time when we would be healed, but all that we received were things that terrified us.
20 Ya Ubangiji, mun gane da muguntarmu da kuma laifin kakanninmu; tabbatacce mun yi maka zunubi.
Yahweh, we admit/know that we are wicked people, and that our ancestors [also] did many wicked things. We have [all] sinned against you.
21 Saboda sunanka kada ka ƙi mu; kada ka ƙasƙantar da kursiyoyinka mai ɗaukaka. Ka tuna da alkawarinka da mu kada ka tā da shi.
But [Yahweh], in order that we may honor [MTY] you, do not despise/abandon us. Do not dishonor [the city where] [MTY] your glorious throne is. [Please] do not forget [us], and do not (break your agreement with us/stop doing what you agreed to do for us).
22 Akwai wani daga cikin gumaka marasa amfani na al’ummai da ya kawo ruwan sama? Sararin sama kansu sukan yi yayyafi? A’a, kai ne, ya Ubangiji Allahnmu. Saboda haka sa zuciyarmu tana a kanka, gama kai ne kake yi wannan duka.
Those idols that [have been brought from] other nations certainly cannot [RHQ] bring rain [to us], and the sky certainly cannot [RHQ] cause rain to fall. Yahweh our God, you are the only one who can do things like that. So we will confidently expect you [to help us].”

< Irmiya 14 >