< Irmiya 14 >

1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya game da fări cewa,
The word of the Lord that came to Jeremiah concerning the words of the drought.
2 “Yahuda tana makoki biranenta suna fama; suna kuka saboda ƙasar, kuka kuma tana tasowa daga Urushalima.
“Judea has mourned. And its gates have fallen and become hard to discern on the ground. And the outcry of Jerusalem has ascended.
3 Manyan mutane suna aika bayinsu su ɗebo ruwa a maɓulɓulai amma babu ruwa. Suka dawo da tulunansu haka nan; da kunya da kuma ƙasƙanci, da kawunansu a rufe.
The greater ones have sent their lesser ones to the water. They went to draw water; they did not find water; they carried their vessels back empty. They were confounded and afflicted, and so they covered their heads.
4 Ƙasa ta tsattsage saboda babu ruwan sama a ƙasar; manoma sun sha kunya suka kuma rufe kawunansu.
Because of the devastation of the earth, because rain did not fall upon the earth, the farmers were confounded; they covered their heads.
5 Har barewa a kurmi ma ta gudu ta bar’ya’yan da ta haihu sababbi saboda babu ciyawa.
For even the doe has given birth in the field, and then left it behind. For there was no grass.
6 Jakan jeji suna tsaye a kan tuddai suna haki kamar diloli; idanunsu sun kāsa gani saboda rashin makiyaya.”
And the wild donkeys stood upon the rocks; like dragons, they drew in the wind, but their eyes failed. For there was no grass.”
7 Ko da yake zunubanmu suna ba da shaida a kanmu, Ya Ubangiji, ka yi wani abu saboda sunanka. Gama jan bayanmu ya yi yawa; mun yi maka zunubi.
“O Lord, if our iniquities have responded against us, let it be for the sake of your name. For our rebellions are many; we have sinned against you.
8 Ya kai, Sa Zuciyar Isra’ila, Mai Cetonsa a lokutan wahala, me ya sa kake yi kamar baƙo a ƙasar, kamar matafiyi wanda yake shirya wuri don yă kwana gari ya waye ya wuce?
O Hope of Israel, its Savior in time of tribulation, why would you be like a sojourner in the land, and like a traveler turning aside for lodging?
9 Me ya sa kake yi kamar mutumin da aka far masa kwasam ba zato, kamar jarumi marar ƙarfin ceto? Kana a cikinmu, ya Ubangiji, da sunanka ake kiranmu; kada ka yashe mu!
Why would you be like a wandering man, like a strong man who is unable to save? But you, O Lord, are with us, and your name is invoked over us, so do not abandon us!”
10 Ga abin da Ubangiji ya ce game da wannan mutane, “Suna son yawace-yawace ƙwarai; ba sa hana ƙafafunsu yawo. Saboda haka Ubangiji bai yarda da su ba; yanzu zai tuna da muguntarsu zai kuma hukunta su saboda zunubansu.”
Thus says the Lord to this people, who have loved to move their feet, and who have not rested, but who have not pleased the Lord: “Now he will remember their iniquities, and now he will visit against their sins.”
11 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Kada ka yi addu’a domin zaman lafiyar mutanen nan.
And the Lord said to me: “Do not choose to pray for this people for good.
12 Ko da yake suna azumi, ba zan saurari kukansu ba, ko da yake suna miƙa hadayun ƙonawa da hadayun gari, ba zan yarda da su ba. A maimako zan hallaka su da takobi, yunwa da annoba.”
When they will fast, I will not heed their petitions. And if they offer holocausts and victims, I will not accept them. For I will consume them by the sword, and by famine, and by pestilence.”
13 Amma na ce, “A, Ubangiji Mai Iko Duka, annabawa sun riƙa ce musu, ‘Ba za ku ga takobi ko ku yi fama da yunwa ba. A maimako, zan ba ku madawwamiyar salama.’”
And I said: “Alas, alas, alas, O Lord God! The prophets are saying to them: ‘You will not see the sword, and there will be no famine among you. Instead, he will give you true peace in this place.’”
14 Sai Ubangiji ya ce mini, “Annabawa suna ta annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba, ban kuma naɗa su ba, ban yi musu magana ba. Suna muku annabci wahayin ƙarya, suna muku duba marar amfani, suna bautar gumaka suna kuma bayyana tunanin kansu ne.
And the Lord said to me: “The prophets prophesy falsely in my name. I did not send them, and I did not instruct them, and I have not spoken to them. They prophesy to you a lying vision, and a divination, and a fraud, and a seduction from their own heart.
15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce game da annabawan da suke annabci da sunana. Ban aike su ba, duk da haka suna cewa, ‘Babu takobi ko yunwar da zai taɓa wannan ƙasa.’ Waɗannan annabawa takobi da yunwa za su hallaka su.
For this reason, thus says the Lord about the prophets who prophesy in my name, whom I have not sent, who say: ‘Sword and famine will not be in this land.’ By sword and famine those prophets will be consumed.
16 Mutanen da suke musu annabcin kuwa za a kore su zuwa titunan Urushalima saboda yunwa da kuma takobi. Babu wanda zai binne su, ko ya binne matansu, ko’ya’yansu maza da mata. Zan aukar musu da masifar da ya dace da su.
And the people, to whom they prophesy, will be cast into the streets of Jerusalem, due to famine and the sword, and there will be no one who may bury them, they and their wives, their sons and daughters, and I will pour out their own evil upon them.
17 “Ka yi musu wannan magana, “‘Bari idanuna su yi ta zub da hawaye dare da rana kada su daina; saboda’yata budurwa, mutanena, sun sha wahalar babban rauni, an yi musu bugu mai ragargazawa.
And you shall speak this word to them: Let my eyes shed tears throughout the night and day, and let them not cease. For the virgin daughter of my people has been crushed by a great affliction, by a very grievous wound.”
18 In na shiga cikin ƙasar, na ga waɗanda takobi ya kashe; in na shiga cikin birni, na ga waɗanda suke fama da yunwa. Da Annabi da firist duk sun tafi ƙasar da ba su sani ba.’”
“If I go out into the fields: behold, those slain by the sword. And if I enter into the city: behold, those weakened by famine. Likewise, the prophet, too, and the priest, have gone into a land that they did not know.
19 Ka ƙi Yahuda ɗungum ke nan? Kana ƙyamar Sihiyona ne? Me ya sa ka buge mu don kada mu warke? Mun sa zuciya ga salama babu abin alherin da ya zo, mun sa rai ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
Could you have utterly cast out Judah? Or has your soul abhorred Zion? Then why have you struck us, so much so that there is no health for us? We have waited for peace, but there is nothing good, and for the time of healing, and behold, trouble.
20 Ya Ubangiji, mun gane da muguntarmu da kuma laifin kakanninmu; tabbatacce mun yi maka zunubi.
O Lord, we acknowledge our impieties, the iniquities of our fathers, that we have sinned against you.
21 Saboda sunanka kada ka ƙi mu; kada ka ƙasƙantar da kursiyoyinka mai ɗaukaka. Ka tuna da alkawarinka da mu kada ka tā da shi.
For the sake of your name, do not give us over into disgrace. And do not dishonor in us the throne of your glory. Remember, do not make void, your covenant with us.
22 Akwai wani daga cikin gumaka marasa amfani na al’ummai da ya kawo ruwan sama? Sararin sama kansu sukan yi yayyafi? A’a, kai ne, ya Ubangiji Allahnmu. Saboda haka sa zuciyarmu tana a kanka, gama kai ne kake yi wannan duka.
Could any of the graven images of the Gentiles send rain? Or are the heavens able to give showers? Have we not hoped in you, the Lord our God? For you have made all these things.”

< Irmiya 14 >