< Ishaya 36 >

1 A shekara ta goma sha huɗu ta mulkin Sarki Hezekiya, Sennakerib sarkin Assuriya ya kai wa dukan birane masu kagaran Yahuda yaƙi ya kuma kame su.
When King Hezekiah had been [ruling Judah] for almost 14 years, King Sennacherib of Assyria came [with his army] to attack the cities in Judah that had walls around them. [They did not conquer Jerusalem, but] they conquered all the other cities.
2 Sai sarkin Assuriya ya aiki sarkin yaƙinsa tare da mayaƙa masu yawa daga Lakish zuwa wurin Sarki Hezekiya a Urushalima. Sa’ad da sarkin yaƙi ya tsaya a wuriyar Tafkin Tudu, a hanya zuwa Filin Mai Wanki,
Then the king of Assyria sent a large army with some of his important officials from Lachish [city] to [persuade] King Hezekiah [to surrender]. When they arrived at Jerusalem, they stood in their positions alongside the aqueduct/channel in which water flows into the upper pool [into Jerusalem], near the road to the field where the women wash clothes.
3 Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci suka fita zuwa wurinsa.
The Israeli officials who went out of the city to talk with them were Hilkiah’s son Eliakim, the (palace administrator/man who supervised the workers in the palace), Shebna the king’s secretary, and Asaph’s son Joah, who wrote down the government decisions.
4 Sai sarkin yaƙin ya ce musu, “Ku faɗa wa Hezekiya. “‘Ga abin da babban sarki, sarkin Assuriya, ya faɗa. A kan me kake dangana wannan ƙarfin halinka?
Then one of Sennacherib’s important officials told them to take this message to Hezekiah: This is what the King of Assyria, the great king, says: “What are you trusting in to rescue you?
5 Ka ce kana da dabara da kuma ƙarfin mayaƙa, amma kana magana banza ce kawai. Ga wa ka dogara, da kake tayar mini?
You say that you have weapons to fight us and some country’s promises [to help you], [and that will enable you to defeat us], but that is only talk [RHQ]. Who do you think will help you to rebel against my [soldiers from Assyria]?
6 Yanzu duba, kana dogara ga Masar, wannan ɗan tsinken kyauron dogarawa, wanda zai soki hannun mutum yă kuma ji masa rauni in ya dangana a kansa! Haka Fir’auna sarkin Masar yake ga duk wanda ya dogara da shi.
Listen to me! You are relying on [the army of] Egypt. But [that will be like] [MET] using a broken reed for a walking stick on which you could lean. [But] it would pierce the hand of anyone who would lean on it! That is what the King of Egypt would be like for anyone who relied on him [for help].
7 Kuma in ka ce mini, “Mun dogara ga Ubangiji Allahnmu ne” ba shi ba ne Hezekiya ya rurrushe masujadan kan tudunsa da bagadansa, yana ce wa Yahuda da Urushalima, “Dole ku yi sujada wa gaban wannan bagade”?
But perhaps you will say to me, ‘[No], we are relying on Yahweh our God [to help us].’ [I would reply], ‘Is he not the one whom [you insulted by] tearing down his shrines and altars and forcing everyone in Jerusalem and [other places in] Judah to worship [only] in front of the altar [in Jerusalem]?’
8 “‘Yanzu fa, bari in yi ciniki da maigidana, sarki Assuriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu, in za ka sa mahaya a kansu!
So I suggest that you make a deal with my master/boss, the king of Assyria. I will give you 2,000 horses, but [I do not think that] you can find 2,000 of your men who can ride on them!
9 Yaya za ka ƙi hafsan mafi ƙanƙanci na hafsoshin maigidana, ko da yake kana dogara ga Masar don kekunan yaƙi da mahayan dawakai?
You are expecting the king of Egypt to send chariots and men riding horses [to assist you]. But they certainly would not [RHQ] be able to resist/defeat even the most insignificant/unimportant official in the army of Assyria!
10 Ban da haka kuma, na zo ne in faɗa in kuma hallaka wannan ƙasa ba tare da Ubangiji ba? Ubangiji kansa ya faɗa mini in tasar wa wannan ƙasa in kuma hallaka ta.’”
Furthermore, [do not think that] [RHQ] we have come here to attack and destroy this land without Yahweh’s orders! It is Yahweh himself who told us to come here and destroy this land!”
11 Sai Eliyakim, Shebna da Yowa suka ce wa sarkin yaƙin, “Ka yi haƙuri ka yi wa bayinka magana da Arameyanci, da yake muna jinsa. Kada ka yi mana magana da Yahudanci a kunnen mutanen da suke kan katanga.”
Then Eliakim, Shebna, and Joah said to the official from Assyria, “Please speak to us in [your] Aramaic language, because we understand it. Do not speak to us in [our] Hebrew language, because the people who are standing on the wall will understand it [and become frightened].”
12 Amma sarkin yaƙin ya amsa ya ce, “Kuna tsammani ga maigidanku da ku ne kawai maigidana ya aiko ni in yi waɗannan maganganu, ba ga mutanen da suke zama a kan katanga ba, waɗanda kamar ku, za su ci kashinsu su kuma sha fitsarinsu?”
But the official replied, “Do you think that my master sent me to say these things [only] to you, and not to the people standing on the wall [RHQ]? [If you reject this message], the [people in this city] will soon need to eat their own dung and drink their own urine, just like you will, [because there will be nothing more for you to eat or drink].”
13 Sa’an nan sarkin yaƙin ya tsaya ya kuma yi kira da Yahudanci ya ce, “Ku ji kalmomin babban sarki, sarkin Assuriya!
Then the official stood up and shouted in the Hebrew language [to the people sitting on the wall]. He said, “Listen to this message from the great king, the King of Assyria!
14 Ga abin da sarki ya ce kada ku bar Hezekiya ya ruɗe ku. Ba zai cece ku ba!
He says, ‘Do not allow Hezekiah to deceive you! He will not be able to rescue you!
15 Kada ku bar Hezekiya ya rarashe ku ku dogara ga Ubangiji sa’ad da ya ce, ‘Tabbatacce Ubangiji zai cece mu; ba za a ba da wannan birni a hannun sarkin Assuriya ba.’
Do not allow him to persuade you to trust in Yahweh, saying that Yahweh will rescue you, and that [the army of] the King of Assyria will never capture this city!’
16 “Kada ku saurari Hezekiya. Ga abin da sarkin Assuriya ya faɗa. Ku nemi salama da ni ku kuma fito zuwa wurina. Ta haka kowa zai ci daga kuringarsa da kuma itacen ɓaurensa ya kuma sha ruwa daga tankinsa,
Do not pay attention to what Hezekiah says! This is what the king [of Assyria] says: ‘Come out of the city and surrender to me. [If you do that, I will arrange for] each of you to drink the juice from your own grapevines and to eat figs from your own trees, and to drink water from your own well.
17 sai na zo na kuma kwashe ku zuwa ƙasa kamar taku, ƙasar hatsi da kuma sabon ruwan inabi, ƙasar abinci da gonakin inabi.
[You will be able to do that] until we come and take you to a land that is like your land—a land where there is grain to make bread and [vineyards to produce grapes for making] new wine and, and where we make lots of bread.’
18 “Kada ku bar Hezekiya ya ruɗe ku sa’ad da ya ce, ‘Ubangiji zai cece mu.’ Allahn wata al’umma ya taɓa ceci ƙasarsa daga hannun sarkin Assuriya?
Do not allow Hezekiah to mislead you by saying, “Yahweh will rescue us.” The gods that people of other nations worship have never [RHQ] rescued any of them from the power [MTY] of the King of Assyria!
19 Ina allolin Hamat da na Arfad? Ina allolin Sefarfayim? Sun fanshi Samariya daga hannuna?
Why were the gods of Hamath and Arpad [cities], and the gods of Sepharvaim unable to rescue Samaria from my power [MTY]?
20 Wanne cikin dukan allolin ƙasashen nan ya iya ceton ƙasarsa daga gare ni? Yaya kuwa Ubangiji zai iya ceci Urushalima daga hannuna?”
No, no god [RHQ] of any nation has been able to rescue their people from me. So why do you think that Yahweh will rescue you people of Jerusalem from my power [MTY]?’”
21 Amma mutanen suka yi shiru ba su kuwa ce kome ba, gama sarki ya yi umarni cewa, “Kada ku amsa masa.”
But the people [who were listening] were silent. No one said anything, because King [Hezekiah] had commanded, “[When the official from Assyria talks to you], do not answer him.”
22 Sai Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, Shebna magatakarda, da kuma Yowa ɗan Asaf marubuci suka tafi wurin Hezekiya, da rigunansu a kyakkece, suka kuwa faɗa masa abin da sarkin yaƙin ya yi ta farfaɗa.
Then Eliakim and Shebna and Joah returned to Hezekiah with their clothes torn [because they were extremely distressed]. They told him what the official from Assyria had said.

< Ishaya 36 >