< Ishaya 35 >

1 Hamada da ƙeƙasasshiyar ƙasa za su yi murna; jeji zai yi farin ciki ya kuma hudo. Kamar fure,
[Some day, it will be as though] the desert [and other very] dry areas are glad [DOU]; the desert will rejoice and flowers will blossom. Like crocuses/daffodils,
2 zai buɗu ya hudo; zai yi farin ciki mai girma ya kuma yi sowa don farin ciki. Za a maido wa Lebanon da darajarta, darajar Karmel da Sharon; za su ga ɗaukakar Ubangiji, darajar Allahnmu.
the desert will produce flowers abundantly; [it will be as though] everything is rejoicing and singing! The deserts will become as beautiful as [SIM] [the trees in] Lebanon, as fertile [SIM] as the plains of the Sharon and Carmel [areas]. [There] people will see the glory of Yahweh; they will see that he is magnificent.
3 Ku ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi, ku ƙarfafa gwiwoyin da suka gaji;
[So], encourage those who are tired and weak.
4 ku faɗa wa waɗanda suka karai a zukata, “Ku yi ƙarfin hali, kada ku ji tsoro; Allahnku zai zo, zai zo domin ya ɗau fansa; da ramuwar Allah zai zo don yă cece ku.”
Say to those who are afraid, “Be strong and do not be afraid, because our God is going to come to get revenge [on his enemies]; he will (pay them back/punish them) for what they have done, and he will rescue you.”
5 Sa’an nan idanun makafi za su buɗe kunnuwan kurame kuma su ji.
When he does that, [he will enable] blind people to see and [enable] deaf people to hear.
6 Sa’an nan guragu za su yi tsalle kamar barewa, bebaye kuma su yi sowa don farin ciki. Ruwa zai kwararo daga jeji rafuffuka kuma a cikin hamada.
Lame people will leap like deer, and those who have been unable to speak will sing joyfully. Water will gush out [from springs] in the desert; streams will flow in the desert.
7 Yashi mai ƙuna zai zama tafki, ƙeƙasasshiyar ƙasa kuma za tă cika da maɓulɓulan rafuffuka. A mazaunin diloli, inda suka taɓa zama, ciyawa da iwa da kyauro za su yi girma.
The very dry ground will become a pool of water, and springs will provide water for the dry land. Grass and reeds and papyrus will grow in places where the jackals/wolves lived previously.
8 Kuma babbar hanya za tă kasance a can; za a ce ta ita Hanyar Mai Tsarki. Marasa tsarki ba za su yi tafiya a kanta ba; za tă zama domin waɗanda suka yi tafiya a wannan Hanya ce; mugaye da wawaye ba za su yi ta yawo a kanta ba.
And there will be a highway through that land; it will be called ‘the Holy Highway’. People who are not acceptable to God will not walk on that road; it will be only for those who conduct their lives as God wants them to; foolish people will become lost while walking on that road.
9 Zaki ba zai kasance a can ba, balle wani naman jeji mai faɗa ya haura kanta; ba za a same su a can ba. Amma fansassu ne kaɗai za su yi tafiya a can,
There will not be any lions there or any other dangerous animals along that road. Only those who have been freed [from being slaves in Babylonia] will walk on it.
10 kuma fansassu na Ubangiji za su komo. Za su shiga Sihiyona da rerawa; matuƙar farin ciki zai mamaye su. Murna da farin ciki za su sha kansu, baƙin ciki kuma da nishi za su gudu.
Those whom Yahweh has freed will return to Jerusalem; they will sing as they enter the city; they will be extremely joyful [MET, PRS] forever. No longer will they be sad or mourn; they will be [completely] joyful [DOU].

< Ishaya 35 >