< Ishaya 35 >

1 Hamada da ƙeƙasasshiyar ƙasa za su yi murna; jeji zai yi farin ciki ya kuma hudo. Kamar fure,
Le désert et le lieu aride se réjouiront, et le lieu solitaire s'égayera, et fleurira comme une rose.
2 zai buɗu ya hudo; zai yi farin ciki mai girma ya kuma yi sowa don farin ciki. Za a maido wa Lebanon da darajarta, darajar Karmel da Sharon; za su ga ɗaukakar Ubangiji, darajar Allahnmu.
Il fleurira abondamment, et s'égayera, s'égayant même et chantant en triomphe. La gloire du Liban lui est donnée, avec la magnificence de Carmel et de Saron, ils verront la gloire de l'Eternel, et la magnificence de notre Dieu.
3 Ku ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi, ku ƙarfafa gwiwoyin da suka gaji;
Renforcez les mains lâches, et fortifiez les genoux tremblants.
4 ku faɗa wa waɗanda suka karai a zukata, “Ku yi ƙarfin hali, kada ku ji tsoro; Allahnku zai zo, zai zo domin ya ɗau fansa; da ramuwar Allah zai zo don yă cece ku.”
Dites à ceux qui ont le cœur troublé; prenez courage, et ne craignez plus; voici votre Dieu; la vengeance viendra, la rétribution de Dieu; il viendra lui-même, et vous délivrera.
5 Sa’an nan idanun makafi za su buɗe kunnuwan kurame kuma su ji.
Alors les yeux des aveugles seront ouverts, et les oreilles des sourds seront débouchées.
6 Sa’an nan guragu za su yi tsalle kamar barewa, bebaye kuma su yi sowa don farin ciki. Ruwa zai kwararo daga jeji rafuffuka kuma a cikin hamada.
Alors le boiteux sautera comme un cerf, et la langue du muet chantera en triomphe; car des eaux sourdront au désert; et des torrents, au lieu solitaire.
7 Yashi mai ƙuna zai zama tafki, ƙeƙasasshiyar ƙasa kuma za tă cika da maɓulɓulan rafuffuka. A mazaunin diloli, inda suka taɓa zama, ciyawa da iwa da kyauro za su yi girma.
Et les lieux qui étaient secs, deviendront des étangs, et la terre altérée [deviendra] des sources d'eaux, et dans les repaires des dragons où ils faisaient leur gîte, il y aura un parvis à roseaux et à joncs.
8 Kuma babbar hanya za tă kasance a can; za a ce ta ita Hanyar Mai Tsarki. Marasa tsarki ba za su yi tafiya a kanta ba; za tă zama domin waɗanda suka yi tafiya a wannan Hanya ce; mugaye da wawaye ba za su yi ta yawo a kanta ba.
Et il y aura là un sentier et un chemin, qui sera appelé le chemin de sainteté; celui qui est souillé n'y passera point, mais il sera pour ceux-là; celui qui va son chemin, et les fous, ne s'y égareront point.
9 Zaki ba zai kasance a can ba, balle wani naman jeji mai faɗa ya haura kanta; ba za a same su a can ba. Amma fansassu ne kaɗai za su yi tafiya a can,
Là il n'y aura point de lion, et aucune de ces bêtes qui ravissent les autres, n'y montera point, et ne s'y trouvera point; mais les rachetés y marcheront.
10 kuma fansassu na Ubangiji za su komo. Za su shiga Sihiyona da rerawa; matuƙar farin ciki zai mamaye su. Murna da farin ciki za su sha kansu, baƙin ciki kuma da nishi za su gudu.
Ceux donc desquels l'Eternel aura payé la rançon, retourneront, et viendront en Sion avec chant de triomphe, et une joie éternelle sera sur leur tête; ils obtiendront la joie et l'allégresse; la douleur et le gémissement s'enfuiront.

< Ishaya 35 >