< Ishaya 31 >
1 Kaiton waɗanda suka gangara zuwa Masar don neman taimako, waɗanda suke dogara ga dawakai, waɗanda suke dogara ga yawan kekunan yaƙinsu da kuma a girman ƙarfin mahayan dawakansu, amma ba sa dogara ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila, ko ya nemi taimako daga Ubangiji.
Woe to those that go down to Egypt for help; and depend for support on horses, and trust on chariots, because they are many; and on horsemen, because they are very strong; but who turn not unto the Holy One of Israel, and seek not the Lord!
2 Shi ma yana da hikima kuma zai iya kawo masifa; ba ya janye kalmominsa. Zai yi gāba da gidan mugu, gāba da waɗanda suke taimakon masu aikata mugunta.
Yet he also is wise, and bringeth evil, and taketh not back his words; and riseth up against the house of evil-doers, and against the help of those that work injustice.
3 Amma Masarawa mutane ne ba Allah ba; dawakansu nama da jini ne ba ruhu ba. Sa’ad da Ubangiji ya miƙa hannunsa, shi da yake taimako zai yi tuntuɓe shi da aka taimaka zai fāɗi; dukansu biyu za su hallaka tare.
But the Egyptians are men, and not God; and their horses are flesh, and not spirit; and the Lord will stretch out his hand, and there shall stumble the helper, and he that is helped shall fall down, and they all shall perish together.
4 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Kamar yadda zaki kan yi ruri babban zaki a kan abin da ya yi farauta, kuma ko da yake dukan ƙungiyar makiyaya sun taru wuri ɗaya a kansa, ba zai jijjigu ta wurin ihunsu ba ko ya damu da kiraye-kirayensu, ta haka Ubangiji Maɗaukaki zai sauko don yă yi yaƙi a kan Dutsen Sihiyona da kuma a kan ƙwanƙolinsa.
For thus hath said the Lord unto me, Just as the lion or the young lion growleth over his prey, against whom is called forth the company of shepherds, of whose voice he is not afraid, and is not depressed because of their multitude: thus will the Lord come down, to fight on mount Zion and on its hill.
5 Kamar tsuntsaye masu shawagi a sama haka Ubangiji Maɗaukaki zai kiyaye Urushalima; zai kāre ta ya kuma fanshe ta, zai ‘ƙetare’ ta ya kuma kuɓutar da ita.”
As fluttering birds, so will the Lord of hosts shield Jerusalem; shielding and delivering; sparing and preserving.
6 Ku dawo gare shi ku da kuka yi masa babban tayarwa, ya Isra’ilawa.
Turn ye unto him from whom the children of Israel have deeply revolted.
7 Gama a wannan rana kowannenku zai ƙi gumakan azurfa da zinariya da hannuwanku masu zunubi suka yi.
For on that day shall every man despise his idols of silver, and his idols of gold, which your own hands have made unto you for a sin.
8 “Za a karkashe Assuriyawa da takobin da ba na yin mutum ba; takobi, da ba na yin mutum ba, zai cinye. Za su gudu daga takobi za a kuma sa samarinsu aikin dole.
Then shall Asshur fall by the sword of one who is not a man; and the sword of one who is not a son of earth shall devour him; and he shall flee him from the sword, and his young men shall become tributary.
9 Kagararsu za tă fāɗi saboda razana; da ganin matsayin yaƙin, shugabannin yaƙinsu za su firgita,” in ji Ubangiji, wanda wutarsa tana a Sihiyona, wanda matoyarsa tana a Urushalima.
And his stronghold shall pass away for fear, and his princes shall be terrified because of the ensign, saith the Lord, who hath a fire in Zion, and a furnace in Jerusalem.