< Ishaya 30 >

1 “Kaiton’ya’ya masu tayarwa,” in ji Ubangiji, “ga waɗanda suke ƙulle-ƙullen da ba nawa ba, suna yin yarjejjeniya, amma ba ta Ruhuna ba, suna jibga zunubi a kan zunubi;
Woe to the rebellious children, saith the Lord, that take counsel, but not from me; and that set themselves a ruler, but not by my spirit, in order that they may add sin to sin:
2 waɗanda suka gangara zuwa Masar ba tare da sun nemi shawarata; waɗanda suke neman taimakon kāriyar Fir’auna, don neman inuwar mafakar Masar.
That travel to go down into Egypt, and have not asked my will; to strengthen themselves through the strength of Pharaoh, and to seek shelter in the shadow of Egypt!
3 Amma kāriyar Fir’auna za tă zama muku abin kunya, inuwar Masar za tă jawo muku kunya.
Therefore shall the strength of Pharaoh become your shame, and the shelter in the shadow of Egypt your disgrace.
4 Ko da yake suna da shugabanni a Zowan kuma jakadunsu sun iso Hanes,
For his princes were at Zo'an, and his ambassadors had reached Chanes.
5 kowa zai sha kunya saboda mutanen da ba su da amfani gare su, waɗanda ba sa taimako ko amfani, sai dai jawo kunya da da-na-sani.”
They all are ashamed because of a people that cannot profit them, neither be a help nor give profit; but [bringeth] shame, and also a reproach.
6 Allah ya faɗa game da dabbobin Negeb cewa, Ta cikin ƙasa mai wahala da mai hatsari inda zakoki da zakanya, inda macizai masu dafi da macizai masu tashi sama suke, jakadu na ɗaukan arzikinsu a kan jakuna, dukiyarsu a kan raƙuma, zuwa ƙasan nan marar riba,
The doom of the beasts of the south: Through the land of trouble and anguish, whence come the lioness and the lion, the viper and flying dragons, they will carry upon the shoulders of young asses their riches, and upon the humps of camels their treasures, to a people that cannot profit.
7 zuwa Masar, wadda taimakonta marar amfani ne. Saboda haka na yi mata laƙabi Rahab Marar Yin Kome.
And the Egyptians will help in vain, and to no purpose; therefore have I called this, Boasters they are in sitting still.
8 Tafi yanzu, ka rubuta musu a kan allo, ka rubuta shi a kan littafi, cewa kwanaki suna zuwa zai zama madawwamin shaida.
Now go, write it before them on a table, and note it in a book, that it may be for the latest time to come, for ever, and to eternity:
9 Waɗannan mutane masu tawaye,’ya’ya masu ruɗu,’ya’yan da ba sa niyya su saurara ga umarnan Ubangiji.
For this is a rebellious people, lying children, children that will not hear the law of the Lord:
10 Sukan ce wa masu gani, “Kada ku ƙara ganin wahayi!” Ga annabawa kuwa sukan ce, “Kada ku ƙara ba mu wahayin abin da yake daidai! Faɗa mana abubuwan da muke so mu ji ne kawai, ku yi annabcin abin da zai ruɗe mu.
Who have said to the seers, Ye shall not see; and to the prophets, Reveal not unto us true things, speak unto us smooth things, reveal deceits;
11 Ku bar wannan hanya, ku tashi daga wannan hanya, ku kuma daina kalubalantarmu da Mai Tsarkin nan na Isra’ila!”
Depart you out of the way, turn aside out of the path, remove from before us the Holy One of Israel.
12 Saboda haka, ga abin da Mai Tsarkin nan na Isra’ila yake cewa, “Saboda haka kun ƙi wannan saƙo, kuka dogara ga aikin kama-karya kuka kuma dogara ga yin ruɗu,
Therefore thus hath said the Holy One of Israel, Because ye despise this word, and trust in oppression and perverseness, and lean thereon for aid:
13 wannan zunubi zai zama muku kamar bango mai tsayi, tsagagge da yake kuma fāɗuwa, da zai rushe nan da nan, ba tsammani.
Therefore shall this iniquity be to you as a threatening breach, swelling out in a high-towering wall, the fall of which will come unawares, suddenly.
14 Zai rushe kucu-kucu kamar tukunyar yumɓu, ya ragargaje ƙaf har cikin gutsattsarinsa ba za a sami ko ɗan katanga don ɗiba garwashin wuta ko a ɗiba ruwa daga tanki ba.”
And he will break it, as one breaketh a potter's vessel, dashing it in pieces without sparing it; so that there cannot be found among its fragments a sherd to rake fire from a hearth and to draw water from a pit.
15 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya faɗa, “Cikin tuba da hutu ne kaɗai cetonku yake, cikin shiru da dogara gare ni ne za ku sami ƙarfinku, amma ba za ku sami ko ɗaya a cikinsu ba.
For thus hath said the Lord Eternal, the Holy One of Israel, In repose and rest shall ye be helped; in quietness and in confidence shall be your strength; and ye would not.
16 Kun ce, ‘A’a, za mu gudu a kan dawakai.’ Saboda haka za ku gudu! Kun ce, ‘Za mu hau dawakai masu sauri mu gudu.’ Saboda haka masu fafararku za su fi ku gudu!
And ye said, “No; for upon horses will we flee;” therefore shall ye flee: and, “Upon swift beasts will we ride;” therefore shall your pursuers be swift.
17 Dubu za su gudu don barazanar mutum guda; da jin barazanar mutane biyar dukanku za ku yi ta gudu sai an bar ku kamar sandar tuta a kan dutse, kamar tuta a kan tudu.”
One thousand [shall flee] at the threatening of one; at the threatening of five shall ye [all] flee: till ye be left as a pole upon a mountain-top, and as an ensign on a hill.
18 Duk da haka Ubangiji yana marmari ya yi muku alheri; ya tashi don yă nuna muku jinƙai. Gama Ubangiji Allah ne mai aikata gaskiya. Masu albarka ne dukanku waɗanda suke dogara gare shi!
And therefore will the Lord wait, to be gracious unto you, and therefore will he exalt himself, to have mercy upon you; for a God of justice is the Lord: happy are all those that wait for him.
19 Ya mutanen Sihiyona, waɗanda suke zama a Urushalima, ba za ku ƙara kuka ba. Zai zama mai alheri sa’ad da kuka yi kukan neman taimako! Da zarar ya ji, zai amsa muku.
For O people of Zion that shall dwell at Jerusalem! thou shalt indeed not weep: he will be surely gracious unto thee at the voice of thy cry; so soon as he heareth it, he answereth thee.
20 Ko da yake Ubangiji yakan ba da abincin azaba da ruwan wahala, ba za a ƙara ɓoye malamanku ba; da idanunku za ku gan su.
And the Lord will give you bread [in] adversity, and water [in] oppression; and thy teachers shall not have to hide themselves in a corner any more, but thy eyes shall see thy teachers:
21 Ko kun juye dama ko hagu, kunnuwanku za su ji murya a bayanku tana cewa, “Ga hanya; ku yi tafiya a kai.”
And thy ears shall hear the word behind thee, saying, “This is the way, walk ye in it,” when ye turn to the right hand, and when ye turn to the left.
22 Sa’an nan za ku ƙazantar da gumakanku da kuka dalaye da zinariya; za ku zubar da su kamar rigar al’adar mace ku kuma ce musu, “Ku ɓace mana da gani!”
And ye will regard as unclean the covering of thy graven idols of silver, and the ornament of thy molten images of gold: thou wilt cast them away as a filthy thing; “Get thee hence,” wilt thou say unto them.
23 Zai kuma aiko muku da ruwan sama don shuki a ƙasa, kuma abincin da zai fito daga gona zai zama mai albarka da kuma mai yawa. A wannan rana shanu za su yi kiwo a wadatacciyar makiyaya.
Then will he give the rain for thy seed, that thou mayest sow in the ground; and bread—the produce of the ground—this shall be fat and nutritious: thy cattle shall feed on that day in extensive pastures.
24 Shanunku da jakunanku da suke huɗar gonakinku za su ci harawa mafi kyau, wanda an sheƙe shi da babban cokali mai yatsu da kuma babban cokali.
The oxen likewise and the young asses that till the ground shall eat salted provender, which hath been winnowed with the shovel and with the fan.
25 A ranar babban kisa, sa’ad da hasumiyoyi za su fāɗi, rafuffukan ruwa za su malalo a kan kowane dutse da kowane tudu mai tsawo.
And there shall be upon every high mountain, and upon every prominent hill, rivulets, streams of waters on the day of the great slaughter, when towers fall.
26 Wata zai yi haske kamar rana, kuma hasken rana zai ma yi sau bakwai na haskenta, kamar hasken cikakku ranaku bakwai, sa’ad da Ubangiji zai ɗaura raunukan mutanensa ya kuma warkar da raunukan da ya yi musu.
And the light of the moon shall be as the light of the sun, and the light of the sun shall be sevenfold, as the light of the seven days, on the day that the Lord bindeth up the broken [limbs] of his people, and healeth the bruise of their wound.
27 Duba, Sunan Ubangiji yana zuwa daga nesa, tare da fushi mai ƙuna da kuma baƙin hayaƙi; leɓunansa sun cika da fushi, harshensa kuma wuta ce mai cinyewa.
Behold, the name of the Lord cometh from afar, burning is his anger, and heavy the smoke; his lips are full of indignation, and his tongue is like a devouring fire;
28 Numfashinsa kamar raƙuman ruwa masu gudu yana tashi har zuwa wuya. Yakan tankaɗe al’ummai cikin lariyar hallaka; yakan sa a muƙamuƙan mutane linzamin da zai jagorance su su kauce.
And his breath, like an overflowing stream, shall reach to the midst of the neck, to toss the nations with the van of falsehood: and [to place] a deceiving bridle on the jaws of the people.
29 Za ku kuma rera kamar a daren da kuke shagalin biki mai tsarki; zukatanku za su yi farin ciki kamar sa’ad da mutane sukan haura da busa zuwa dutsen Ubangiji, zuwa Dutse na Isra’ila.
[Then] shall ye have a song, as in the night when a festival is ushered in, and joy of heart, as when one goeth with the flute to come unto the mountain of the Lord, to the Rock of Israel.
30 Ubangiji zai sa mutane su ji muryarsa mai daraja ya kuma sa su ga hannunsa na saukowa tare da fushi mai ƙuna da kuma wuta mai cinyewa, gizagizai za su ɓarke, za a yi hadarin tsawa da ƙanƙara.
And the Lord will cause his majestic voice to be heard, and will show the stretching down of his arm, in the indignation of [his] anger, and in the flame of a devouring fire, in flood, and tempest, and stones of hail.
31 Muryar Ubangiji za tă firgita Assuriya da sandar mulkinsa zai kashe su.
For because of the voice of the Lord shall be terrified Asshur, that smote [you] with the rod.
32 Kowane bugun da Ubangiji zai yi musu da bulalarsa na hukunci zai zama kiɗi ga ganguna da garaya, yayinda yake yaƙi da su da naushin hannunsa.
And at every passage of the appointed staff which the Lord will let fall on him, there shall be [music] on tambourine and harp; and in the tumult of battles will he fight with them.
33 An riga an shirya wurin ƙonawa; an shirya shi saboda sarki. An haƙa ramin wutarsa da zurfi da kuma fāɗi, da isashen wuta da itacen wuta; numfashin Ubangiji, yana kamar kibiritu mai ƙuna, da aka sa masa wuta.
For already of old is Topheth made ready; also this is prepared for the king—deep and wide; its pile hath fire and wood in plenty, the breath of the Lord, like a stream of sulfur, will kindle it into a flame.

< Ishaya 30 >